Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da ƙudirin dokar kafa ‘yansandan jihohi.
An yanke wannan hukunci ne a ranar Alhamis yayin zaman majalisar da kakakinta, Tajudeen Abbas, ya jagoranta.
Jimillar ‘yan majalisa 292 ne suka kaɗa ƙuri’a, inda 288 suka goyi bayan ƙudirin, yayin da huɗu ne kawai suka yi adawa da ƙudirin.
Saboda tsarin ƙaɗa ƙuri’a na na’ura bai yi aiki ba, an yi amfani da ɗaga hannu wajen kaɗa ƙuri’ar.
Ƙudirin na nufin inganta tsaro a Nijeriya ta hanyar bai wa jihohi damar kafa ‘yansandansu, tare da na tarayya.
Haka kuma, ya fayyace yadda za a raba ayyuka da tsarin aiki tsakaninsu.
‘Yan majalisa sun ce an shafe watanni ana tattaunawa da gudanar da shawarwari a sassa daban-daban na ƙasar kafin a kai ga wannan mataki.
Majalisar Dattawa ma ta fara ɗaukar matakin kan ƙudirin, inda ta tura shi kwamitin gyaran kundin tsarin mulki domin ƙarin nazari, sannan za a kaɗa ƙuri’a ta ƙarshe a nan gaba.















Discussion about this post