ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

by Sadiq
49 minutes ago

Majalisar Dattawa ta amince da tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin shekarar 2025 da wata uku, inda aka mayar da ranar ƙarshe daga 30 ga watan Yuni zuwa 30 ga watan Satumba, 2026.

An yanke wannan hukunci ne a ranar Alhamis bayan sanatoci sun tattauna kan jinkirin aiwatar da wasu ayyuka da kuma yadda ake amfani da kuɗaɗen da aka riga aka sakar wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati.

Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Tahir Monguno, ya ce har yanzu ana gudanar da ayyuka da dama kuma suna buƙatar ƙarin lokaci saboda jinkirin saye da samar da kayayyaki, matakan gudanarwa da sauran ƙalubalen aiwatar da ayyuka.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa idan ba a tsawaita wa’adin ba, akwai yiwuwar a dakatar da wasu muhimman ayyuka, a yi asarar kuɗaɗen gwamnati da aka riga aka ware, tare da kawo cikas ga shirye-shiryen gwamnati.

Shugaban Kwamitin Kasafi na Majalisar Dattawa, Sanata Solomon Adeola, ya ce tsawaitawar ta shafi ɓangaren ayyukan raya ƙasa ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

Ya ƙara da cewa har yanzu akwai wasu ayyuka da biyan kuɗaɗe da ba a kammala ba a ƙarƙashin kasafin 2025, wanda ya sa aka ga dacewar ƙara lokaci.

Sanatocin sun amince da ƙudirin gaba ɗaya, sannan Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da cewa sabon wa’adin aiwatar da kasafin zai ƙare ne a ranar 30 ga watan Satumba, 2026.

Ya ce matakin zai taimaka wajen tabbatar da kammala ayyukan da ake yi da kuma ci gaba da biyan kuɗaɗen da suka dace ba tare da tangarɗa ba.

A baya, Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta riga ta tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2025 zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Wannan sabon ƙarin lokaci zai bai wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati damar kammala ayyukan da suke yi tare da amfani da kuɗaɗen da aka amince da su yadda ya kamata.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
Manyan Labarai

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

June 11, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa
Manyan Labarai

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
Next Post
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

June 11, 2026
Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

June 11, 2026
Za A Kammala Aikin Bututun Iskar Gas Na AKK A Disambar 2024 – NNPC

Na Yi Matuƙar Mamakin Sammaci A Kaina – Mele Kyari

June 11, 2026
inec

INEC: APC da LP Ne Kaɗai Suka Cancanci Shiga Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kebbi

June 11, 2026
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

June 11, 2026
An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

June 10, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.