Majalisar Dattawa ta amince da tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin shekarar 2025 da wata uku, inda aka mayar da ranar ƙarshe daga 30 ga watan Yuni zuwa 30 ga watan Satumba, 2026.
An yanke wannan hukunci ne a ranar Alhamis bayan sanatoci sun tattauna kan jinkirin aiwatar da wasu ayyuka da kuma yadda ake amfani da kuɗaɗen da aka riga aka sakar wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati.
Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Tahir Monguno, ya ce har yanzu ana gudanar da ayyuka da dama kuma suna buƙatar ƙarin lokaci saboda jinkirin saye da samar da kayayyaki, matakan gudanarwa da sauran ƙalubalen aiwatar da ayyuka.
Ya bayyana cewa idan ba a tsawaita wa’adin ba, akwai yiwuwar a dakatar da wasu muhimman ayyuka, a yi asarar kuɗaɗen gwamnati da aka riga aka ware, tare da kawo cikas ga shirye-shiryen gwamnati.
Shugaban Kwamitin Kasafi na Majalisar Dattawa, Sanata Solomon Adeola, ya ce tsawaitawar ta shafi ɓangaren ayyukan raya ƙasa ne kawai.
Ya ƙara da cewa har yanzu akwai wasu ayyuka da biyan kuɗaɗe da ba a kammala ba a ƙarƙashin kasafin 2025, wanda ya sa aka ga dacewar ƙara lokaci.
Sanatocin sun amince da ƙudirin gaba ɗaya, sannan Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da cewa sabon wa’adin aiwatar da kasafin zai ƙare ne a ranar 30 ga watan Satumba, 2026.
Ya ce matakin zai taimaka wajen tabbatar da kammala ayyukan da ake yi da kuma ci gaba da biyan kuɗaɗen da suka dace ba tare da tangarɗa ba.
A baya, Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta riga ta tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2025 zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.
Wannan sabon ƙarin lokaci zai bai wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati damar kammala ayyukan da suke yi tare da amfani da kuɗaɗen da aka amince da su yadda ya kamata.















Discussion about this post