ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

by Sadiq
2 months ago

Majalisar Dattawa ta amince da tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin shekarar 2025 da wata uku, inda aka mayar da ranar ƙarshe daga 30 ga watan Yuni zuwa 30 ga watan Satumba, 2026.

An yanke wannan hukunci ne a ranar Alhamis bayan sanatoci sun tattauna kan jinkirin aiwatar da wasu ayyuka da kuma yadda ake amfani da kuɗaɗen da aka riga aka sakar wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati.

Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Tahir Monguno, ya ce har yanzu ana gudanar da ayyuka da dama kuma suna buƙatar ƙarin lokaci saboda jinkirin saye da samar da kayayyaki, matakan gudanarwa da sauran ƙalubalen aiwatar da ayyuka.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa idan ba a tsawaita wa’adin ba, akwai yiwuwar a dakatar da wasu muhimman ayyuka, a yi asarar kuɗaɗen gwamnati da aka riga aka ware, tare da kawo cikas ga shirye-shiryen gwamnati.

Shugaban Kwamitin Kasafi na Majalisar Dattawa, Sanata Solomon Adeola, ya ce tsawaitawar ta shafi ɓangaren ayyukan raya ƙasa ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Ya ƙara da cewa har yanzu akwai wasu ayyuka da biyan kuɗaɗe da ba a kammala ba a ƙarƙashin kasafin 2025, wanda ya sa aka ga dacewar ƙara lokaci.

Sanatocin sun amince da ƙudirin gaba ɗaya, sannan Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da cewa sabon wa’adin aiwatar da kasafin zai ƙare ne a ranar 30 ga watan Satumba, 2026.

Ya ce matakin zai taimaka wajen tabbatar da kammala ayyukan da ake yi da kuma ci gaba da biyan kuɗaɗen da suka dace ba tare da tangarɗa ba.

A baya, Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta riga ta tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2025 zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Wannan sabon ƙarin lokaci zai bai wa ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati damar kammala ayyukan da suke yi tare da amfani da kuɗaɗen da aka amince da su yadda ya kamata.

MASU ALAKA

Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Next Post
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.