Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na samun rancen haɗin gwiwa na dala miliyan 516.3 domin aikin Babbar Hanyar Sokoto zuwa Badagry, bayan nazari da amincewa da rahoton kwamitinta a zaman majalisar.
Amincewar ta biyo bayan wata wasiƙa da shugaban ƙasa ya aika ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026, inda ya nemi sahalewar majalisa domin karɓar bashi daga ƙasashen waje bisa tanade-tanaden dokar ofishin hukumar kula da lamuni na shekarar 2011 da kuma dokar tsimi da tanadi Fiscal ta 2007.
An miƙa buƙatar ga Kwamitin Majalisar Dattawa kan Basussuka na Cikin Gida da Ƙasashen Waje a ranar 23 ga Afrilu, 2026, wanda daga bisani ya gabatar da rahotonsa, inda ya amimce da shawarar amso bashin.
Da yake gabatar da rahoton a madadin shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Wamakko (Sokoto ta Arewa), Sanata Adamu Aliero (Kebbi ta Tsakiya) ya bayyana cewa za a yi amfani da kuɗin wajen aikin Sashe na Ɗaya, Mataki na Ɗaya (A da B1) na aikin hanyar, wanda ya ƙunshi kusan kilomita 120 daga cikin babban aikin da ake sa ran zai kai kusan kilomita 1,000 daga Sokoto zuwa Badagry.
Ya ƙara da cewa, an tsara aikin ne domin inganta ababen more rayuwa a ƙasa ta hanyar haɗa jihohin Sokoto, Kebbi, Neja, Kwara, Oyo, Ogun da Legas, wanda hakan zai inganta kasuwanci, sauƙaƙa sufuri, da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.















Discussion about this post