Tawagar kwararrun jami’an kiwon lafiya ta kasar Sin, wadda ta isa jamhuriyar dimokaradiyyar Congo ko kuma DRC a takaice, ta gana da shugaban cibiyar nazarin kwayoyin halittu ta DRC Jean-Jacques Muyembe, don tattauna matakan hadin gwiwa na shawo kan cutar Ebola dake addabar kasar.
Yayin ganawar tasu a jiya Laraba, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi dangane da halin da ake ciki game da yaduwar cutar a halin yanzu, da muhimman matakan kandagarki da shawo kanta, da matakan gwaje-gwaje, da jinya da sauran sassan hadin gwiwa na inganta kiwon lafiyar jama’a.Cikin jawabinsa mista Muyembe, ya ce Sin na da matukar kwarewa a fannin shirya tsarin kiwon lafiyar jama’a, da shawo kan cututtuka masu yaduwa, da samar da jinyar cututtuka, don haka yake fatan karfafa hadin gwiwa na zahiri don inganta ikon tunkarar annobar ta Ebola.
A nasa tsokacin kuwa, shugaban tawagar kwararrun ta Sin Lu Ming, cewa ya yi sun isa DRC ne domin karfafa tattaunawa, da tsare-tsare tare da hukumomin lafiya na DRC, da cibiyoyin lafiya, da na yaki da cututtuka, da cibiyoyin bincike gwargwadon ainihin bukatun kasar.
Lu ya kara da cewa, tawagarsa za ta samar da tallafi a fannin karfafa sanin makamar aiki, a tsarin yaki da cutar da DRC ke gudanarwa, da aiki tare da takwarorinsu na DRC wajen gaggauta shawo kan bazuwar annobar.
Wata sanarwa da cibiyar Africa CDC ta fitar a ranar Talata, ta yi kira da kasashen nahiyar da su gaggauta nazarta, da karfafa da aiwatar da matakan tantance jama’ar dake fita daga kasashe daban daban, da aiwatar da matakan kula da lafiya a dukkanin filayen jiragen sama, da tashoshin ruwa, da manyan iyakokin kasa, da nufin dakile bazuwar annobar ta Ebola. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post