Wani mai bincike game da harkokin shari’a dan kasar Afirka ta kudu Nkanyiso Ngqulunga, ya ce manufar kasar Sin ta kawar da daukacin harajin fito ga kasashen Afirka 53 da take da huldar diflomasiyya da su, za ta haifar da fadadar hada-hadar fitar da hajojin nahiyar zuwa kasashen ketare, tare da ingiza sabon kuzari ga hadin gwiwar cinikayya tsakanin kasashen nahiyar da kasar Sin.Nkanyiso Ngqulunga, ya bayyana hakan ne kwanan nan yayin wata zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua.
Yana mai cewa kawar da harajin zai bude sabbin damammaki na bunkasa fannoni da dama, ciki har da noma, da sarrafa hajojin masana’antu da sauransu.Masanin ya kara da cewa tasirin fadadar hada-hadar tattalin arzikin kasar Sin, na kara sauya salon yanayin cinikayyar kasa da kasa, a gabar da kasashen Afirka ke kokarin saita alkiblar su don cin gajiyar kasuwar kasar Sin wadda ke kara bunkasa.
An ayyana ranar daya ga watan Mayu dake tafe a matsayin lokacin fara aiki da sabuwar manufar kawar da harajin na Sin ga kasashen Afirka, a wani yunkuri na fadada burin Sin na karfafa hadin gwiwar tattalin arziki tare da kasashen Afirka, da ingiza ci gaban bai daya, yayin da yanayin cinikayyar duniya ke kara sauyawa.
Kazalika, manufar na da nufin fadada hada-hadar cinikayya, da ingiza zuba jari tsakanin Sin da kasashen Afirka, da samar da managartan kafofi na fitar da hajojin Afirka zuwa sassan ketare. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post