Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin sakin Sheikh Sani Abdulkadir Zaria ba tare da wani sharadi ba, tare da ba shi diyyar Naira miliyan 5 sakamakon take haƙƙoƙinsa na ɗanAdam da hukumomin tsaro da wani banki suka yi.
A hukuncin da Mai Shari’a Peter O. Lifu ya yanke a ranar Litinin, kotun ta bayyana cewa tsare malamin na tsawon lokaci ba tare da ingantaccen umarnin kotu ba ya karya haƙƙoƙinsa na mutunci, ‘yancin kai, adalci a shari’a, da ‘yancin zirga-zirga, kamar yadda Kundin Tsarin Mulki na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) da Yarjejeniyar Afirka kan Haƙƙin Dan Adam suka tanada.
A cikin takardar hukuncin da aka tabbatar, an bayyana cewa an shigar da ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/55/2026 ƙarƙashin dokar kare haƙƙin ɗanAdam ta 2009, inda Sheikh Zaria ya kai ƙara kan wasu hukumomi guda biyar da suka haɗa da EFCC, da DIA, da Babban Lauyan Tarayya, da Jaiz Bank Plc, da kuma SSS.
Mai Shari’a Lifu ya umarci Babban Lauyan Tarayya da ya tabbatar da cikakken bin umarnin kotun.
Kotun ta kuma umarci a saki wanda ya shigar da ƙarar nan take ba tare da wani sharadi ba.















Discussion about this post