Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa ya kamata Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ji tsoron shan kaye a zaɓen 2027, domin zai fafata ne da miliyoyin ‘yan Nijeriya da suka fuskanci matsananciyar wahala a ƙarƙashin gwamnatinsa.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta yi wannan bayani ne a matsayin martani ga kalaman Shugaban Ƙasa da ya ce ba ya jin tsoron ‘yan adawa, har ma ya yi musu ba’a da cewa, suna gudanar da manyan tarukansu a kan titi.
Sai dai ADC ta bayyana kalaman a matsayin waɗanda ba su dace da shugaban ƙasa ba, tana mai cewa da irin waɗannan furuci, shugaban yana nuna ya fi mayar da hankali kan siyasa alhali mafi yawan ‘yan Nijeriya na ƙara nutsewa cikin talauci, tare da zama cikin halin rashin tsaro daga hannun ‘yan tada ƙayar baya da masu garkuwa da mutane.
Da take mayar da martani ga kalaman shugaban, ADC ta ce: “Abin da ‘yan Nijeriya suka fahimta ya zuwa yanzu, shi ne, ba wata kwarin gwiwa ga shugaba Tinubu, abin da suke gani kawai, rashin tsaro, da tsadar rayuwa wanda miliyoyin ‘yan ƙasa ke ciki.
”Ta ƙara da cewa a lokacin da iyalai ke fama da tsadar rayuwa mai tsanani, da hauhawar farashin abinci, shugaban ya zaɓi yin ba’a ga ‘yan adawa maimakon magance matsalolin jama’a.
Kakakin jam’iyyar ya kuma nuna cewa a daidai lokacin da shugaban ke wannan magana, aka samu rahotannin sace yara daga cibiyoyin rubuta jarrabawa.















Discussion about this post