Mataimakin Kwamishinan ‘Yansanda mai kula da harkokin Kuɗi da Gudanarwa a Rundunar ‘Yansandan Jihar Legas, Khan Salihu, ya rasu.
Kakakin rundunar, SP Ambimbola Adebisi ne, ya sanar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, inda ya ce Salihu ya rasu a ranar 15 ga watan Yunin 2026.
Adebisi ya bayyana marigayin a matsayin jajirtaccen jami’in ɗansanda wanda ya yi aiki da ƙwazo, aminci da gaskiya wajen hidimta wa Rundunar ‘Yansandan Nijeriya.
Ya ce marigayin ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen tafiyar da harkoki da inganta ayyukan rundunar a Jihar Legas.
Ya ƙara da cewa rasuwarsa ta girgiza jami’ai da sauran ma’aikatan rundunar, tare da bayyana ta a matsayin babban rashi.
Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Legas, Tijani Olaiwola Fatai, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalai, abokai, abokan aiki da masoyan marigayin a madadin ɗaukacin jami’an rundunar.















Discussion about this post