Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya soki hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya ba da umarnin soke rijistar jam’iyyar da wasu jam’iyyun siyasa a Nijeriya.
Obi ya ce ya kamata a soke wannan hukunci, yana mai gargaɗin cewa irin wannan mataki na iya rage amincewar jama’a ga tsarin shari’a da cibiyoyin dimokiraɗiyya a ƙasar.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a ranar Litinin, ya ce ƙasashe masu ƙarfi suna dogara ne da amincewa ga doka da oda, inda ya ƙara da cewa yawancin ‘yan Najeriya ba sa yadda da cibiyoyin ƙasar.
Ya ce rashin tabbas a tsarin shari’a na hana masu zuba jari, har ma yana sa wasu kasuwanni su fi dogaro da kotunan ƙasashen waje maimakon na Nijeriya.
Obi ya kuma yi kira ga alƙalai da lauyoyi da su tsaya tsayin daka wajen kare doka da tsarin dimokiraɗiyya, yana mai cewa dole ne ‘yan ƙasa su kasance suna da tabbacin samun adalci a kotuna.
Ya bayyana cewa Nijeriya na iya sake gina amincewar jama’a da kuma cimma ci gaban dimokiraɗiyya idan aka kare cibiyoyinta yadda ya kamata.















Discussion about this post