Mahalarta taron masu ruwa da tsaki dangane da hada-hadar zuba jari na Gauteng, wanda ya gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu a kwanan baya, sun yi hasashen yadda matakin janye dukkanin harajin kwastam kan hajojin kasashen Afirka da ake shigarwa kasuwannin Sin, zai taimaka wajen bunkasa cinikayya da tattalin arzikin kasashen nahiyar.
Da yake tsokaci game da hakan, babban jami’in shirin “Proudly South African”, wani shiri dake rajin ingiza sayayyar hajoji da hidimomi da ake samarwa a cikin Afirka ta kudu, mista Eustace Mashimbye, ya ce matakin na gwamnatin kasar Sin, zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci a kasar, da ma raya tattalin arzikin dukkanin kasashen Afirka. Mashimbye ya ce “Manufar Sin ta janye harajin za ta yi matukar amfanar ‘yan kasuwar Afirka ta kudu, kuma hakan dama ce da kasashen nahiyar suka jima suna jira”.
Kazalika, Mashimbye ya ce manufar za ta bude managartan kofofi na shiga kasuwa mafi girma a duniya, tare da samar da damammaki na hakika, wadanda za su haifar da ci gaba, da bunkasa masana’antu, da guraben ayyukan yi a dukkanin sassan Afirka.
A nasa bangare kuwa, babban jakada a ofishin jakadancin Sin dake birnin Johannesburg Pan Qingjiang, cewa ya yi ana sa ran manufar za ta yi matukar bunkasa cinikayya, da yaukaka alakar tattalin arziki tsakanin Sin da Afirka. Ya ce a gabar da Sin ke kara azamar aiwatar da manufar yafe dukkanin harajin kwastam ga kasashen Afirka, Sin da Afirka ta kudu na kuma aiwatar da tsare-tsare na kut-da-kut, don tabbatar da nasarar manufar, da cimma cikakkiyar gajiya daga gare ta.
Bugu da kari, jami’in ya ce manufar za ta samar da gagarumin alfanu ga al’ummun Afirka, yayin da su kuma masu sayayya na Sin, za su ci gajiyar karin hajoji masu inganci daga kasashen Afirka. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post