Wasu mazauna Dutse a jihar Jigawa sun bukaci a haramta harkar caca gaba daya domin kare kansu daga asarar kudi tare da inganta tarbiyyar mallakar kudade cikin hikima a tsakanin matasa.
Haka kuma sun nuna damuwa kan yawaitar cibiyoyin caca a yankin tare da kira ga hukumomi da su dauki matakan gaggawa domin magance matsalar.
Wannan na kunshe ne cikin ra’ayoyi daban-daban da wasu daga cikin mazauna yankin suka bayyana a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya yi da su ranar Lahadi a Dutse.
Wani mazaunin yankin, Malam Ibrahim Musa, ya danganta yawaitar harkar caca da jahilci da kuma son samun kudi cikin sauki.
Musa ya ce ya yi asarar kusan naira miliyan uku sakamakon caca, yana mai cewa wannan dabi’a na taimakawa wajen karuwar aikata laifuka a tsakanin matasa.
Ya bayyana cewa da dama daga cikin masu yin cacar na zaman gidan yari a halin yanzu saboda laifukan da suka shafi narkewar kudi a harkar caca.















Discussion about this post