Sau tari wasu matan suna zaƙewa akan a sake su ba tare da tsayawa sunyi tunani ko nazari mai zurfi da zai hanasu yin kuskuren da za suyi dana sani ba.
Ana samu wasu matan da tabbas ya dace su nemi saki. Wasu kuwa kwata kwata bai dace ba amma kuma sai su nemi yin hakan saboda rashin tsayawa sunyi dogon nazari.
Kamin ki biyewa zuciyarki data raya miki neman saki, to fa ya kamata ki yiwa kanki waɗannan tambayoyin kamar haka:
1. Kina son mijin ki? Wannan shi ne abu na farko da ya kamata ki soma neman amsar sa da kanki domin ta hakan ne idan kin saku baza ki yi danasi ba.
2. Wani irin laifi ne? Dole ne ki duba nauyin laifin da kike tuhumar mijinki da shi ya kai ki nemi saki ko dai kawai ranki ne ya ɓaci.
Sau dayawa wasu matan suna neman saki ne akan yar ƙaramar matsalar da za a iya haƙuri dashi a zamantakewa na aure.
3. Yaya iyayyenki za su ji? Kamin ki nemi saki ya zama dole ki samu amsar yadda iyayyenki za su ji bayan mutuwar auren naki.
Iyaye ko waliyai suna iya hanaki jin daɗin zaman zawarci muddin basu goyi bayan mutuwar aurenki ba. Don haka ya zame miki wajibi ki soma samun amsar wannan matsalar kamin ki nemi saki.
4. Makomar yaranki? : Idan kuna da haihuwa a tsakaninku da mijin naki, ya zama wajibi ki samu amsar makomar ƴaƴanki da wannan mijin naki kamin ki bukaci ya sake ki.
Akwai mata da yawa da suke neman saki bayan an sake su kuma matsalar yaran da suka bari ya zame masu matsalar rashin kwanciyar hankali. Don haka dole ki samo amsar makomar ƴaƴanki kamin ma ki cewa miji ka sake ni.
5. Sabuwar Rayuwa? Kamin ki buɗe baki kice a sake ki, ki samu amsar yadda zaki fuskanci sabuwar rayuwar da za ki shiga ba kuma bayan an sake ki ba ki riƙa bin tsohon mijin na ki kina neman taimakon sa.
Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da ɗaukar ɗawainiyar kanki koda kina da masu miki baza su miki yadda miji zai miki ba.
Dole ne ki samu amsar wajen da za ki zauna ko da kuwa kina da mazauni zai bambamta da zaman gidan miji.
Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da kare kanki kamar yadda aure ya rufa miki asiri.
Waɗannan sune wasu daga cikin tambayoyin da ya kamata duk mace mai neman saki ta soma samun amsar su kamin tayi azarɓaɓin neman a saketa.
Shi dai zaman aure da haƙuri ne da kuma kau da kai. Duk matsalar da kike fuskanta a gidan mijinki da har kike neman saki akansa, wata na can tana haƙuri da matsalar data fi taki.
Ma’aurata a riƙa haɗawa da haƙuri. Mata a daina neman saki cikin fushi ba tare da duban abubuwan da zasu je su dawo ba. Allah Ya bamu haƙurin zama da juna.















Discussion about this post