ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

by Bilkisu Tijjani
1 month ago

Sau tari wasu matan suna zaƙewa akan a sake su ba tare da tsayawa sunyi tunani ko nazari mai zurfi da zai hanasu yin kuskuren da za suyi dana sani ba.

Ana samu wasu matan da tabbas ya dace su nemi saki. Wasu kuwa kwata kwata bai dace ba amma kuma sai su nemi yin hakan saboda rashin tsayawa sunyi dogon nazari.

Kamin ki biyewa zuciyarki data raya miki neman saki, to fa ya kamata ki yiwa kanki waɗannan tambayoyin kamar haka:

ADVERTISEMENT

1. Kina son mijin ki? Wannan shi ne abu na farko da ya kamata ki soma neman amsar sa da kanki domin ta hakan ne idan kin saku baza ki yi danasi ba.

2. Wani irin laifi ne? Dole ne ki duba nauyin laifin da kike tuhumar mijinki da shi ya kai ki nemi saki ko dai kawai ranki ne ya ɓaci.

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Sau dayawa wasu matan suna neman saki ne akan yar ƙaramar matsalar da za a iya haƙuri dashi a zamantakewa na aure.

3. Yaya iyayyenki za su ji? Kamin ki nemi saki ya zama dole ki samu amsar yadda iyayyenki za su ji bayan mutuwar auren naki.

Iyaye ko waliyai suna iya hanaki jin daɗin zaman zawarci muddin basu goyi bayan mutuwar aurenki ba. Don haka ya zame miki wajibi ki soma samun amsar wannan matsalar kamin ki nemi saki.

4. Makomar yaranki? : Idan kuna da haihuwa a tsakaninku da mijin naki, ya zama wajibi ki samu amsar makomar ƴaƴanki da wannan mijin naki kamin ki bukaci ya sake ki.

Akwai mata da yawa da suke neman saki bayan an sake su kuma matsalar yaran da suka bari ya zame masu matsalar rashin kwanciyar hankali. Don haka dole ki samo amsar makomar ƴaƴanki kamin ma ki cewa miji ka sake ni.

5. Sabuwar Rayuwa? Kamin ki buɗe baki kice a sake ki, ki samu amsar yadda zaki fuskanci sabuwar rayuwar da za ki shiga ba kuma bayan an sake ki ba ki riƙa bin tsohon mijin na ki kina neman taimakon sa.

Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da ɗaukar ɗawainiyar kanki koda kina da masu miki baza su miki yadda miji zai miki ba.

Dole ne ki samu amsar wajen da za ki zauna ko da kuwa kina da mazauni zai bambamta da zaman gidan miji.

Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da kare kanki kamar yadda aure ya rufa miki asiri.

Waɗannan sune wasu daga cikin tambayoyin da ya kamata duk mace mai neman saki ta soma samun amsar su kamin tayi azarɓaɓin neman a saketa.

Shi dai zaman aure da haƙuri ne da kuma kau da kai. Duk matsalar da kike fuskanta a gidan mijinki da har kike neman saki akansa, wata na can tana haƙuri da matsalar data fi taki.

Ma’aurata a riƙa haɗawa da haƙuri. Mata a daina neman saki cikin fushi ba tare da duban abubuwan da zasu je su dawo ba. Allah Ya bamu haƙurin zama da juna.

Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Next Post
Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.