ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

by Bilkisu Tijjani
2 weeks ago

Sau tari wasu matan suna zaƙewa akan a sake su ba tare da tsayawa sunyi tunani ko nazari mai zurfi da zai hanasu yin kuskuren da za suyi dana sani ba.

Ana samu wasu matan da tabbas ya dace su nemi saki. Wasu kuwa kwata kwata bai dace ba amma kuma sai su nemi yin hakan saboda rashin tsayawa sunyi dogon nazari.

Kamin ki biyewa zuciyarki data raya miki neman saki, to fa ya kamata ki yiwa kanki waɗannan tambayoyin kamar haka:

ADVERTISEMENT

1. Kina son mijin ki? Wannan shi ne abu na farko da ya kamata ki soma neman amsar sa da kanki domin ta hakan ne idan kin saku baza ki yi danasi ba.

2. Wani irin laifi ne? Dole ne ki duba nauyin laifin da kike tuhumar mijinki da shi ya kai ki nemi saki ko dai kawai ranki ne ya ɓaci.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

Sau dayawa wasu matan suna neman saki ne akan yar ƙaramar matsalar da za a iya haƙuri dashi a zamantakewa na aure.

3. Yaya iyayyenki za su ji? Kamin ki nemi saki ya zama dole ki samu amsar yadda iyayyenki za su ji bayan mutuwar auren naki.

Iyaye ko waliyai suna iya hanaki jin daɗin zaman zawarci muddin basu goyi bayan mutuwar aurenki ba. Don haka ya zame miki wajibi ki soma samun amsar wannan matsalar kamin ki nemi saki.

4. Makomar yaranki? : Idan kuna da haihuwa a tsakaninku da mijin naki, ya zama wajibi ki samu amsar makomar ƴaƴanki da wannan mijin naki kamin ki bukaci ya sake ki.

Akwai mata da yawa da suke neman saki bayan an sake su kuma matsalar yaran da suka bari ya zame masu matsalar rashin kwanciyar hankali. Don haka dole ki samo amsar makomar ƴaƴanki kamin ma ki cewa miji ka sake ni.

5. Sabuwar Rayuwa? Kamin ki buɗe baki kice a sake ki, ki samu amsar yadda zaki fuskanci sabuwar rayuwar da za ki shiga ba kuma bayan an sake ki ba ki riƙa bin tsohon mijin na ki kina neman taimakon sa.

Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da ɗaukar ɗawainiyar kanki koda kina da masu miki baza su miki yadda miji zai miki ba.

Dole ne ki samu amsar wajen da za ki zauna ko da kuwa kina da mazauni zai bambamta da zaman gidan miji.

Dole ne ki samu amsar yadda za ki ci gaba da kare kanki kamar yadda aure ya rufa miki asiri.

Waɗannan sune wasu daga cikin tambayoyin da ya kamata duk mace mai neman saki ta soma samun amsar su kamin tayi azarɓaɓin neman a saketa.

Shi dai zaman aure da haƙuri ne da kuma kau da kai. Duk matsalar da kike fuskanta a gidan mijinki da har kike neman saki akansa, wata na can tana haƙuri da matsalar data fi taki.

Ma’aurata a riƙa haɗawa da haƙuri. Mata a daina neman saki cikin fushi ba tare da duban abubuwan da zasu je su dawo ba. Allah Ya bamu haƙurin zama da juna.

Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Amfanin Man Kwakwa Guda 11

MASU ALAKA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Uwargida Sarautar Mata

Ko Kin San…Yadda Za Ki Zauna Da Mijinki Mai Mata Fiye Da Daya?

May 10, 2026
Next Post
Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

Ana Tuhumar Mutum Biyu Kan Dala 461,600 Da Suka Yi Ɓatan Dabo A Filin Jirgin Saman Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.