Kungiyar ‘Yan Asalin Jihar Kebbi Mazauna Abuja, wato ‘Association Of Kebbi State Indiginous Residents In Abuja’, (AKIRA) ta kaddamar da zaben sabbin shugabanninta.
Da yake gabatar da jawabi ga manema labarai jim kadan bayan kammala zaben, sabon zababben shugaban kungiyar Abubakar Abdullahi (A.A), ya godewa wa Allah madaukakin Sarki da ya ba shi wannan nasara. “Ina godiya ga Allah da nuna mana wannan rana da aka gudanar da wannan zabe, wanda hakika an yi zabe kamar yadda kake gani Alhamdu Lillahi, mun gode wa Allah bisa wannan ni’imar da ya yi mana. Yanzu abin da za mu sa a gaba shi ne hangen yadda za mu sake ciyar da wannan kungiyar gaba musamman ga ‘yan Jihar Kebbi domin kai wa wani mataki fiye da wanda take kai yanzu,” in ji shi.
Sannan ya bayyana irin hazakar tsohon shugaban kungiyar Alhaji Isa Usman Tsando Kangiwa, wanda ya yi a karkashinsa a matsayin mataimaki shekaru kusan hudu, don haka a karkashin wannan mun samu nasara sosai. “Domin gwamnatin Jihar Kebbi ta nuna mana halacci a matsayinta na gwamnati wanda mu da muke zaune a Abuja ba ta manta da mu ba ta yi mana alhairai da dama domin a halin yanzu kamar yadda ka fada ina cikin S.A na Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi Dakta Nasir Idris Kauran Gwadu, don haka an samu ci gaban da ba zai lissafu ba, kuma muna yi masa godiya” in ji shi.
Shi ma a nasa bangaren tsohon shugaban kungiyar Alhaji Isa Usman Tsando Kangiwa, nuna farin ciki ya yi da godiya ga Allah, inda ya ce “Allah ya nuna musu farkon wannan jagoranci lafiya yau kuma ga shi an zo lokacin da suka sauka suka ba wa wasu.“ Yau an gabatar da zabe na ajiye shugabanci na ba wa mataimakina kuma zai dora daga inda na tsaya in sha Allahu.
Domin a lokacin da muka karbi jagorancin wannan kungiya muna ta kokarin ganin mun kan al’umma wuri daya, cikin ikon Allah da yardarsa Allah ya ba mu iko da dama muka samu kan al’ummarmu ya hadu, wanda a bisa wannan dukkan wani dan kuniya da shiga wani Ibtila’i in dai ba na aikata miyagun laifi bane, wannan kungiya na kokarin ganin ta karbo shi, ”in ji shi.
Ya kara da cewa, a karkashin jagorancinsa ne aka yi wa wannan kungiya rajista, kuma shi ne ya bude mata a susu kuma a karkashin jagorancinsa ne ya samar mata shugaban yanki a nan Abuja wanda akalla akwai shugabbannin yankuna akalla 30 a nan Abuja.“A Jagorancina Gwamnan Jihar Kebbi ya tallafa wa wannan kungiya da kudi Naira miliyan 100, kuma mun yi amfani da su wanjen tallafawa yan wannan kungiya kananan yan kasuwa domin su dogara da kansu, kuma mun tabbatar cewa abubuwa na tafiya daidai.
Shi ko Sakataren Kungiyar na Kasa Murtala Yahaya Ambursa, wanda tsohon sakatare ne kuma zababbe a yanzu, cewa ya yi a duk lokacin da ka yi aiki kuma aka yaba da hazakarka, mutane za su bukaci ka sake dawowa, wanda hakan ne ya kasance kuma ga shim un dawo, kuma za mu dora in sha Allahu fiye da wanda muka yi a baya.
“Mun samu nasarori da ba zaku misultu ba, daga ciki akwa samun alakar mabobinmu da gwamnatin tarayya da ta jiha, gwamnati na jawo mu a jiki, gwamnatin jiharmu ta bamu matsayin S.A na gwamna mutum 20, ta ba mu wasu mukamai na mutum 10, kuma kowannensu yana nan akan aikinsa, to wannan ba karamin ci gaba bane”.
Sabbin shugabannin dai su ne; Tsohon Mataimakin Shugaban Kungiyar Abubakar Abdullahi (A.A), a matsayin sabon shugaba. Sai kuma Auwal Isiyaku Gulma a matsayin mataimaki, yayin da Murtala Yahaya ya matsayinsa na Sakataren kungiyar na Kasa, sai kuma Mahmuda Muhd a matsayin Sakataren Tsare-tsare, Kabiru Ibrahim Koko, Sakataen Kudi, Sulaiman Umar kuma Ma’aji, da kuma Kakakin kungiyar Musa Rabiu. Sauran sun hada da Muhammad Aliyu, Daraktan jin dadin jama’a da Walwala, sai shugabar Mata Hajiya Nafisa Abdulmumin.














