Yayin da duniya ke bikin Ranar Kasa da Kasa ta Mutanen da Suka bace, iyalai a fadin Arewa maso Gabashin Nijeriya na ci gaba da rayuwa cikin radadi da rashin tabbas saboda rashin sanin inda ’yan uwansu suke.
Sabbin alkaluma daga Kwamitin Kasa da Kasa na Red Cross (ICRC) sun nuna cewa sama da mutum 17,000 ne aka yi wa rajista a matsayin wadanda suka bace a Nijeriya, da kuma sama da kashi 90 cikin 100 na al’amuran ke da alaka da rikicin makamai da tayar da kayar baya a Arewa maso Gabas, da kuma ayyukan ’yan bindiga da garkuwa da mutane da yawa a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya.
Daga cikin adadin, an samu kusan 9,000 a Jihar Borno, 3,000 a Adamawa, sannan 2,500 a Yobe, wanda ya sa adadin mutanen da suka bace a jihohin Arewa maso Gabas uku ya kai kusan 14,500.
Tayar da kayar baya na ci gaba da kasancewa babban dalilin bacewar mutane a yankin, lamarin da ya jefa dubban iyalai cikin yanayi na tsakanin fata da jimami.
A bayan wadannan alkaluma akwai iyaye, ’yan’uwa da sauran dangi wadanda suka shafe shekaru suna neman ’yan uwansu da suka bace a lokacin da rikicin Boko Haram ya yi kamari.
Binciken Daily Trust ya nuna cewa iyalai da dama sun shafe shekaru cikin azaba da damuwa, yayin da wasu kuma suka rasa ’yan hotuna da kayayyakin amfanin yau da kullum na wadanda suka bace, wadanda za su taimaka musu wajen adana tunaninsu.
Ga Kashim Mohammed, radadin rasa kanwarsa ta wajen uba mai shekaru 30, Falmata Mohammed, har yanzu yana da zafi kamar yadda ya faru shekaru 14 da suka gabata.
Falmata da mahaifiyarta sun yanke shawarar barin Maiduguri zuwa Fatakwal bayan sun gaji da hare-haren Boko Haram da ke maimaituwa. Sai dai ta bace a yayin tafiyar.
Bayan shekaru, jita-jita da bayanan shaidun gani da ido sun nuna cewa wata kungiyar masu aikata laifi ce ta yi garkuwa da ita, sannan suka wuce da ita ta haye wani kogi zuwa wajen iyaka.
Daga baya iyalan suka samu dan haske na fata, bayan wani mai ba da bayanai ya ce ya ga Falmata da rai. Sai dai mai ba da bayanin ya rasu kafin ya samu damar bayar da karin bayani, lamarin da ya katse hanya daya tilo da iyalan suke da ita wajen gano ta.
Mohammed ya sake fuskantar wani babban rashi lokacin da ambaliyar ruwa ta ranar 11 ga Satumba, wadda ta yi barna sosai a Maiduguri, ta kwashe wani akwati na karfe da ke dauke da hotunan Falmata tun daga yarintarta har zuwa lokacin da ta girma.
Da yake babu sauran hotunanta, yanzu ya dogara ne da tunaninsa wajen tuna kamanninta da kuma halin karamcinta.
Ya ce, “Ina tuna lokacin da nake makaranta, ta sayar da talabijin dinta, ta ba ni dukkan kudin da ta samu, sannan ta karfafa mini gwiwa in ci gaba da karatu.
“Ita ce ’yar fari ta uwar gidanmu. Ba zan taba mantawa da wannan ba,” in ji Mohammed.
Farin cikin Mahaifiya Ya Kare
Hajja Yakura Abatcha ta rasa sauyi a rayuwarta har abada shekaru 12 da suka gabata, lokacin da Boko Haram ta kai hari garin Baga.
Yayin da iyalai ke tserewa zuwa Chadi ta hanyar kwale-kwale, Yakura ta rasa ’ya’yanta uku Habu mai shekara takwas, Abba mai shekara 10, da Aisha mai shekara tara.
Bayan shekaru, wata bakuwa daga Baga ta ba ta dan haske, inda ta ce ta ga wata yarinya mai kama da Aisha a Darussalam, Chadi.
Matar ta karbi hoton karshe da Yakura ke da shi na ’yarta, sannan ta yi mata alkawarin taimaka mata wajen gano inda take. Sai dai matar ta bace ba tare da wata alama ba, tare da hoton.
Rashin mijinta da ’ya’yanta uku ya jefa Yakura cikin matsanancin yanayin damuwa ta fuskar kwakwalwa da tunani.
Ta ce, “Bayan ’yan makonni, na rasa hankalina, kuma da kyar nake iya tuna ko gane wani abu.”
Duk da cewa ’yan uwanta sun taimaka mata ta farfado, daga baya ta sake yin aure, amma ta sake zama bazawara.
Ta ce addu’ar da take yi a kullum har yanzu ita ce: “Abin da nake rokon Allah kawai shi ne ya sake hada ni da ’ya’yana, ko kuma ya gafarta musu idan sun rasu.”
“Na yi kuka har sai da na makance”
Ba Modu Ali shi ma ya rayu cikin radadin rasa ’yarsa da ya fi so, Adama mai shekaru 13, wadda ’yan ta’addan Boko Haram suka yi garkuwa da ita a Gambarou Zanna Ari sama da shekaru goma da suka wuce.
Shaidun gani da ido sun shaida masa cewa ’yan tawayen sun dora bindiga a kan mahaifiyar yarinyar, wato matarsa, kafin su tafi da Adama.
Ali ya ce wannan mummunan lamari da kuma tsawon lokacin da ya yi cikin jimami sun shafi ganinsa.
Ya ce, “Na yi kuka har sai da na makance. Yanzu da kyar nake iya ganin hannuna, amma radadin har yanzu sabo ne a zuciyata. A koyaushe ina tuna murmushinta mai taushi da kusancin da ke tsakanina da ita.”
Maryamu Daniel, wata bazawara mai zaman makoki, ita ma ta shafe shekaru 13 tana neman danta da ya bace, Yunana.
Ta ce an yi garkuwa da danta ne yayin da yake noma tare da dan’uwansa.
Ta tuna cewa, “An yi garkuwa da Yunana yayin da yake noma tare da dan’uwansa.”
Ta ce dan’uwansa ya samu damar tserewa, amma aka tafi da Yunana.
Ta ce, “Na rika kiran lambar wayarsa sau da dama, ina addu’ar a ji ringing, amma shiru kawai nake ji daga wajensa. Har zuwa yau, binciken yana ci gaba. Har yanzu muna neman sa, muna rike da duk wani fata da ya rage mana.”
Maryamu ta nuna godiya ga ICRC bisa kokarin da take yi na gano mutanen da suka bace, amma ta yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen neman mutanen da suka bace.
Eli Zanna Saleh yana neman ’yarsa mai shekaru 20, Bebilo Zanna, da kuma ’yar’uwarsa mai shekaru 26, wadanda suka bace yayin wani harin Boko Haram da aka kai Mayenti, wani gari da ke Karamar Hukumar Bama ta Jihar Borno.
Saleh ya ce harin ya tilasta wa mazauna garin tserewa zuwa cikin daji, yana mai cewa Bebilo ta yi aure ne kwanan nan.
Ya ce, “Harin ya faru ne a lokacin wannan rikici, kuma suka gudu zuwa cikin daji tare da ’yar’uwata, wadda ita ma a baya ta rasa mijinta sannan ta sake yin aure. Tun daga wannan mummunan ranar, ba mu samu ko wani bayani guda daya game da inda suke ko kuma ko har yanzu suna raye ba.”
Ya ce rashin sanin halin da suke ciki ya sa yake cikin fargaba a kodayaushe, musamman a duk lokacin da ya ji labarin cewa iyalan ’yan Boko Haram ko mutanen da aka yi garkuwa da su sun mika wuya ga sojoji.
Ya ce, “Ko a yanzu da muke magana, na samu labarin cewa wasu mata da suka mika wuya ana tsare da su a Bama. Ina shirin tafiya can nan take domin duba ko a karshe zan iya gano su.”
Saleh ya kuma yi nadamar rashin samun hotunan ’yan uwansa da suka bace, domin adana tunaninsu idan har aka tabbatar da cewa sun rasu.














