Ga kasashen da kasar Japan ta kaiwa hare-hare, ranar 31 ga watan Yuli, wadda aka hade a lamba “731”, na wakiltar laifuffukan da Japan ta aikata a yayin yakin duniya. Shekaru 81 da kawo karshen yakin duniya na biyu, a ranar 31 ga watan Yuli, gwamnatin kasar Japan ta kafa hukumar leken asiri ta kasar a hukunce, tare da gudanar da taron majalisar leken asiri ta kasar a karon farko, wanda firaministar kasar Takaichi Sanae ta shugabanta. Wani abun tambaya a nan shi ne ko mene ne manufar kasar Japan ta yin hakan? Wannan ne karo na farko da kasar Japan ta kafa tsarin leken asiri na kasar, tun bayan yakin duniya na biyu.
Manazarta sun yi nuni da cewa, gwamnatin kasar Japan ta yi amfani da dalilin kiyaye tsaron kasa ne domin raya karfin leken asiri, da koyo, da kafa tsarin tattara bayanai a yayin yakin, da sa kaimi ga farfado da ra’ayin nuna karfin tuwo na kasar, da yunkurin fadada karfin soja da shirya makamai, lamarin da zai haifar da bazarana ga zaman lafiya da zaman karko a yankin.
Bisa aya ta 9 ta kundin tsarin mulki na zaman lafiya na kasar Japan, an tsara cewa, kasar Japan za ta yi watsi da tada duk wani irin yaki bisa ikonta, da kuma yin watsi da amfani da karfin tuwo wajen daidaita rikicin kasa da kasa, da hana ta kafa karfin soja na sama da ruwa da kasa, da kuma kin amincewa da ikonta na yin yaki. Amma a halin yanzu, gwamnatin kasar Japan tana shiri, da daukar matakan sabawa alkawarinta.
Masu ra’ayin rikau na kasar Japan, suna farfado da aikin leken asiri, wanda hakan ya sabawa odar kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu. Don haka ya kamata sassan kasa da kasa su mayar da hankali kan batun, da daukar matakai don hana yaduwar sabon ra’ayin amfani da karfin tuwo na kasar Japan, da kuma tabbatar da odar kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu baki daya. (Zainab Zhang)














