• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan tsawon watanni biyu, kasashen Nijar da Amurka sun cimma daidaito game da batun janyewar sojojin kasar Amurka daga Nijar din, inda a ranar 19 ga watan nan, ma’aikatun tsaro na kasashen biyu suka fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, Amurka za ta janye sojojinta daga Nijar kafin ranar 15 ga watan Satumba mai zuwa. 

Idan ba a manta ba, ba da jimawa ba, wato a karshen bara, Faransa ta janye sojojinta daga Nijar bisa bukatar Nijar din.

  • Xi Ya Taya Murnar Bude Tattaunawar Manyan Jami’An Sin Da Amurka a Fannin Yawon Shakatawa Karo Na 14
  • Ba Wanda Zai Iya Keta Ka’Idar “Kasar Sin Daya Tak a Duniya” 

To, ko me ya sa Nijar ke ta korar sojojin kasashen yamma daga kasar? Lallai za mu iya gano amsar tambayar daga tattaunawar da firaministan kasar Ali Mahamane Lamine Zeine ya yi tare da wakilin jaridar Washington Post a kwanan baya.

A watan Maris na bana, wata tawagar wakilan kasar Amurka karkashin jagorancin Molly Phee, mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka, ta ziyarci jamhuriyar Nijar, kuma tawagar ba ta jima ba da barin kasar, sai Nijar ta sanar da yin watsi da yarjejeniyar hadin gwiwar ayyukan soja da ta kulla da Amurka. A game da haka, Mr. Lamine Zeine ya ce, a yayin ziyararta, Madam Molly Phee ta yi wa gwamnatin Nijar barazana da cewa, idan Nijar ta daddale yarjejeniyar sayar da Uranium ga Iran, to, za a kakaba mata takunkumi. Mr. Lamine Zeine ya kara da cewa, “kun zo nan kasarmu kun yi mana barazana, abu ne da ba za mu amince da shi ba, kuma kun zo nan kun bayyana mana da wa ya kamata mu yi hulda, shi ma abu ne da ba za mu amince da shi ba……a lokacin da ‘yan ta’adda suka zo suna kashe jama’armu tare da kone garuruwanmu, su Amurkawa suna nan a kasarmu, amma kallo kawai suke yi. Sun zo sun bar ‘yan ta’adda suna kai mana hare-hare yadda suka ga dama, wannan ba abu ne na sada zumunta ba. Mu muka ga yadda Amurka ta yi kokarin kare kawayenta irinsu Ukraine da Isra’ila”.

Alal hakika, akasarin al’ummun kasar Nijar na ganin cewa, neman tabbatar da iko a kan ma’adinan Uranium da Allah ya albarkaci Nijar da shi, na daga cikin dalilan da suka sa kasashen Amurka, da Faransa suka girke sojojinsu a kasar, hakan abun yake ma a sauran wasu kasashen Afirka wadanda suke da arzikin mai da sauran ma’adinai.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

A cikin shekaru 10 da suka wuce, Amurka, da Faransa sun fake da sunan yakar ta’addanci, wajen girke sojojinsu a yankin Sahel na nahiyar Afirka, sai dai hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta kara fama da talauci da rikici. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don neman tsoma baki cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne kasashen yamma suke girke sojojinsu, don haka ma suka yi ta nuna kin jinin sojojin. Ba ma kawai a Nijar ba, Faransa ta janye sojojinta daga kasashen Mali da Burkina Faso a cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. A watan Afrilun bana, Chadi ita ma ta bukaci Amurka ta janye sojojinta daga kasar.

A sa’i daya kuma, kasancewar kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka a galibin kasashen Afirka, kasashen Afirka na ganin kasashen yamma na yunkurin ci gaba da samun iko a nahiyar da ke da arzikin albarkatu iri iri, duba da cewa barazana ce a maimakon kwanciyar hankali, sojojin da kasashen yamma suka tura suka haifar ga nahiyar, kuma tarnaki a maimakon ci gaba ne gudummawarsu ta samar. Yadda aka kori sojojin Amurka da na Faransa ma ya bayyana yadda kasashen Afirka suke kyamar “sabon nau’in mulkin mallaka” da kasashen yamma suke neman kafawa, da ma bukatunsu na neman samun ‘yancin kansu, da hadin gwiwar cin moriyar juna.

Ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin da suka yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaBoxingLiu Qiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Wanda Zai Iya Keta Ka’Idar “Kasar Sin Daya Tak a Duniya” 

Next Post

Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

2 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

3 days ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

4 days ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 week ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

2 weeks ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Next Post
Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.