ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Bayan tsawon watanni biyu, kasashen Nijar da Amurka sun cimma daidaito game da batun janyewar sojojin kasar Amurka daga Nijar din, inda a ranar 19 ga watan nan, ma’aikatun tsaro na kasashen biyu suka fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, Amurka za ta janye sojojinta daga Nijar kafin ranar 15 ga watan Satumba mai zuwa. 

Idan ba a manta ba, ba da jimawa ba, wato a karshen bara, Faransa ta janye sojojinta daga Nijar bisa bukatar Nijar din.

  • Xi Ya Taya Murnar Bude Tattaunawar Manyan Jami’An Sin Da Amurka a Fannin Yawon Shakatawa Karo Na 14
  • Ba Wanda Zai Iya Keta Ka’Idar “Kasar Sin Daya Tak a Duniya” 

To, ko me ya sa Nijar ke ta korar sojojin kasashen yamma daga kasar? Lallai za mu iya gano amsar tambayar daga tattaunawar da firaministan kasar Ali Mahamane Lamine Zeine ya yi tare da wakilin jaridar Washington Post a kwanan baya.

ADVERTISEMENT

A watan Maris na bana, wata tawagar wakilan kasar Amurka karkashin jagorancin Molly Phee, mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka, ta ziyarci jamhuriyar Nijar, kuma tawagar ba ta jima ba da barin kasar, sai Nijar ta sanar da yin watsi da yarjejeniyar hadin gwiwar ayyukan soja da ta kulla da Amurka. A game da haka, Mr. Lamine Zeine ya ce, a yayin ziyararta, Madam Molly Phee ta yi wa gwamnatin Nijar barazana da cewa, idan Nijar ta daddale yarjejeniyar sayar da Uranium ga Iran, to, za a kakaba mata takunkumi. Mr. Lamine Zeine ya kara da cewa, “kun zo nan kasarmu kun yi mana barazana, abu ne da ba za mu amince da shi ba, kuma kun zo nan kun bayyana mana da wa ya kamata mu yi hulda, shi ma abu ne da ba za mu amince da shi ba……a lokacin da ‘yan ta’adda suka zo suna kashe jama’armu tare da kone garuruwanmu, su Amurkawa suna nan a kasarmu, amma kallo kawai suke yi. Sun zo sun bar ‘yan ta’adda suna kai mana hare-hare yadda suka ga dama, wannan ba abu ne na sada zumunta ba. Mu muka ga yadda Amurka ta yi kokarin kare kawayenta irinsu Ukraine da Isra’ila”.

Alal hakika, akasarin al’ummun kasar Nijar na ganin cewa, neman tabbatar da iko a kan ma’adinan Uranium da Allah ya albarkaci Nijar da shi, na daga cikin dalilan da suka sa kasashen Amurka, da Faransa suka girke sojojinsu a kasar, hakan abun yake ma a sauran wasu kasashen Afirka wadanda suke da arzikin mai da sauran ma’adinai.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A cikin shekaru 10 da suka wuce, Amurka, da Faransa sun fake da sunan yakar ta’addanci, wajen girke sojojinsu a yankin Sahel na nahiyar Afirka, sai dai hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta kara fama da talauci da rikici. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don neman tsoma baki cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne kasashen yamma suke girke sojojinsu, don haka ma suka yi ta nuna kin jinin sojojin. Ba ma kawai a Nijar ba, Faransa ta janye sojojinta daga kasashen Mali da Burkina Faso a cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. A watan Afrilun bana, Chadi ita ma ta bukaci Amurka ta janye sojojinta daga kasar.

A sa’i daya kuma, kasancewar kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka a galibin kasashen Afirka, kasashen Afirka na ganin kasashen yamma na yunkurin ci gaba da samun iko a nahiyar da ke da arzikin albarkatu iri iri, duba da cewa barazana ce a maimakon kwanciyar hankali, sojojin da kasashen yamma suka tura suka haifar ga nahiyar, kuma tarnaki a maimakon ci gaba ne gudummawarsu ta samar. Yadda aka kori sojojin Amurka da na Faransa ma ya bayyana yadda kasashen Afirka suke kyamar “sabon nau’in mulkin mallaka” da kasashen yamma suke neman kafawa, da ma bukatunsu na neman samun ‘yancin kansu, da hadin gwiwar cin moriyar juna.

Ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin da suka yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.