ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasashen Afirka Suke Ta Korar Sojojin Kasashen Yamma?

by CGTN Hausa
2 years ago
Afirka

Bayan tsawon watanni biyu, kasashen Nijar da Amurka sun cimma daidaito game da batun janyewar sojojin kasar Amurka daga Nijar din, inda a ranar 19 ga watan nan, ma’aikatun tsaro na kasashen biyu suka fitar da hadaddiyar sanarwar cewa, Amurka za ta janye sojojinta daga Nijar kafin ranar 15 ga watan Satumba mai zuwa. 

Idan ba a manta ba, ba da jimawa ba, wato a karshen bara, Faransa ta janye sojojinta daga Nijar bisa bukatar Nijar din.

  • Xi Ya Taya Murnar Bude Tattaunawar Manyan Jami’An Sin Da Amurka a Fannin Yawon Shakatawa Karo Na 14
  • Ba Wanda Zai Iya Keta Ka’Idar “Kasar Sin Daya Tak a Duniya” 

To, ko me ya sa Nijar ke ta korar sojojin kasashen yamma daga kasar? Lallai za mu iya gano amsar tambayar daga tattaunawar da firaministan kasar Ali Mahamane Lamine Zeine ya yi tare da wakilin jaridar Washington Post a kwanan baya.

ADVERTISEMENT

A watan Maris na bana, wata tawagar wakilan kasar Amurka karkashin jagorancin Molly Phee, mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka, ta ziyarci jamhuriyar Nijar, kuma tawagar ba ta jima ba da barin kasar, sai Nijar ta sanar da yin watsi da yarjejeniyar hadin gwiwar ayyukan soja da ta kulla da Amurka. A game da haka, Mr. Lamine Zeine ya ce, a yayin ziyararta, Madam Molly Phee ta yi wa gwamnatin Nijar barazana da cewa, idan Nijar ta daddale yarjejeniyar sayar da Uranium ga Iran, to, za a kakaba mata takunkumi. Mr. Lamine Zeine ya kara da cewa, “kun zo nan kasarmu kun yi mana barazana, abu ne da ba za mu amince da shi ba, kuma kun zo nan kun bayyana mana da wa ya kamata mu yi hulda, shi ma abu ne da ba za mu amince da shi ba……a lokacin da ‘yan ta’adda suka zo suna kashe jama’armu tare da kone garuruwanmu, su Amurkawa suna nan a kasarmu, amma kallo kawai suke yi. Sun zo sun bar ‘yan ta’adda suna kai mana hare-hare yadda suka ga dama, wannan ba abu ne na sada zumunta ba. Mu muka ga yadda Amurka ta yi kokarin kare kawayenta irinsu Ukraine da Isra’ila”.

Alal hakika, akasarin al’ummun kasar Nijar na ganin cewa, neman tabbatar da iko a kan ma’adinan Uranium da Allah ya albarkaci Nijar da shi, na daga cikin dalilan da suka sa kasashen Amurka, da Faransa suka girke sojojinsu a kasar, hakan abun yake ma a sauran wasu kasashen Afirka wadanda suke da arzikin mai da sauran ma’adinai.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A cikin shekaru 10 da suka wuce, Amurka, da Faransa sun fake da sunan yakar ta’addanci, wajen girke sojojinsu a yankin Sahel na nahiyar Afirka, sai dai hakan bai haifar da da mai ido ba, ganin yadda kasashen suka yi ta kara fama da talauci da rikici. Abin da ya sa karin al’ummar kasashen Afirka suka gane cewa, don neman tsoma baki cikin harkokin gidansu, da kwace albarkatunsu ne kasashen yamma suke girke sojojinsu, don haka ma suka yi ta nuna kin jinin sojojin. Ba ma kawai a Nijar ba, Faransa ta janye sojojinta daga kasashen Mali da Burkina Faso a cikin ‘yan shekarun baya bayan nan. A watan Afrilun bana, Chadi ita ma ta bukaci Amurka ta janye sojojinta daga kasar.

A sa’i daya kuma, kasancewar kasashen yamma sun taba yin mulkin mallaka a galibin kasashen Afirka, kasashen Afirka na ganin kasashen yamma na yunkurin ci gaba da samun iko a nahiyar da ke da arzikin albarkatu iri iri, duba da cewa barazana ce a maimakon kwanciyar hankali, sojojin da kasashen yamma suka tura suka haifar ga nahiyar, kuma tarnaki a maimakon ci gaba ne gudummawarsu ta samar. Yadda aka kori sojojin Amurka da na Faransa ma ya bayyana yadda kasashen Afirka suke kyamar “sabon nau’in mulkin mallaka” da kasashen yamma suke neman kafawa, da ma bukatunsu na neman samun ‘yancin kansu, da hadin gwiwar cin moriyar juna.

Ya kamata kasashen yamma su gane cewa, lokacin da suka yi wa kasashen Afirka duk abin da suka ga dama tuni ya wuce. Dole ne a bi ka’idar martaba juna, da zaman daidaito, da cin moriyar juna wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, sabo da ta haka ne za a kai ga tabbatar da ci gaba, da tsaro na bai daya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.