ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Wakar Mahakar Tagulla Ta Chambishi Ke Samun Farin Jini

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 week ago
Chambishi

Yau ita ce Ranar Afirka, ranar da ke tunawa da samun ’yancin kan al’ummun kasashen Afirka daga mulkin mallaka, wadda kuma ke dauke da burin ’yan Afirka na fita daga talauci da zamanantar da kasashensu. Jama’a, a wannan rana ta musamman, ina so in gabatar muku wata waka da ta yi matukar samun farin jini ta yanar gizo kwanan nan, tare da labarin da ke cikinta. Wakar da ma’aikatan Kamfanin NFCA(Non-Ferrous Company-Africa Mining) da ke Zambiya suka rera ita ce “Wakar Mahakar Tagulla ta Chambishi”. “Down, then up again…” wakar ba kawai ta ba da labarin farfadowar wannan mahakar tagulla mai tsawon tarihi na sama da shekaru 100 ba, har ma ta nuna hadin gwiwa da cin gajiyar juna tsakanin Sin da Afirka.

Turawan Ingila ’yan mulkin mallaka ne suka gano mahakar tagulla ta Chambishi a shekarar 1899, kuma mahakar ta dan bunkasa a hannunsu, amma saboda matsalolin fasaha da gudanarwa, aikin hakar tagulla a wurin ya tsaya cik a shekarun 1980. Daga nan, kamfanonin kasashen yamma suka tafi da ribar da suka ci, suka bar mahakar da ma’aikatanta da rashin aikin yi. A shekarar 1998, kamfanin CNMC(China Nonferrous Metal Mining) ya je wajen mahakar tare da jari, fasaha da kuma zumunta, kuma ya daidaita matsalolin da a baya Turawan suka kasa magancewa tare da farfado da mahakar, har ma ya gina mahakar dijital irinta ta farko a Afirka, inda aka kai ga gudanar da ayyukan hakawa da lodawa da kuma jigila, da injuna da fasahohin kirkirarriyar basira, matakin da ya yi matukar inganta ayyukan ma’aikatan. A lokaci guda, CNMC ya dogara ga mahakar Chambishi wajen fadada masana’antu masu alaka, ciki har da samar da injuna da harhada sinadarai da jigilar kayayyaki da sauransu, inda ya gina yankin masana’antu, baya ga kafa yankin hadin gwiwar tattalin arziki da kasuwanci na Sin da Zambiya, wanda ya jawo kusan kamfanoni 100, don kara inganta tsarin manasana’antu a kasar. A cikin shekaru 20 da suka wuce, kamfanin CNMC ya zuba jarin da yawansa ya kai sama da dala biliyan 1.6 ga mahakar, kuma ya biya harajin dala miliyan 578, baya ga samar da guraben ayyukan yi sama da 6,200. Ban da haka, ya kuma inganta ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya da ci gaban al’ummar garin Chambishi. Abin lura kuma shi ne, a lokacin da yawancin kamfanonin hakar ma’adinai a Zambiya suka dakatar ko rage aikinsu sakamakon matsalar hada-hadar kudi ta duniya da ta kunno kai a shekarar 2008, CNMC ya cika alkawarinsa na “ba za mu rage aikin hakar tagulla ko ton daya ba, kuma ba za mu kori ma’aikaci ko daya ba, kuma ba za mu rage zuba jari ba”, wanda ya tsaya tsayin daka tare da al’ummar wurin don tinkarar kalubalen da suke fuskanta. Don haka tsohon shugaban kasar Zambiya, marigayi Edgar Lungu, ya bayyana CNMC a matsayin “abin koyi ga masu zuba jari na kasashen waje”.

Mahakar Chambishi wani misali ne na hadin gwiwar Sin da Afirka. Da layin dogo na Mombasa zuwa Nairobi a Kenya, da layin dogo mai kwarin daukar nauyi na farko a hamada da ke kasar Aljeriya, da kuma tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Najeriya, kasar Sin ta taimaka wajen gina manyan ayyukan more rayuwa masu yawa a fadin Afirka, wadanda suka inganta hadewa da juna a tsakanin sassan nahiyar da ma sauran sassan duniya, baya ga bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasashen. Har ila yau, daga samar da fasahar noman da ake kira Juncao wajen taimaka wa makiyaya a Mauritania kiwon tumaki, zuwa dakin gwaje-gwajen hadin gwiwa na rigakafin cututtuka da kiwon lafiyar jama’a tsakanin Sin da Tanzaniya, zuwa kawar da gaba dayan harajin fito kan kayayyaki daga kasashen Afirka 53 da ke da huldar diflomasiyya da kasar Sin, hadin gwiwar Sin da Afirka a fannoni daban daban, yana kyautata rayuwar al’ummar kasashe daban daban a Afirka.

ADVERTISEMENT

“Steel in the silence, the town stays alive…Chambishi Copper Mine, Rise again, rise again…”,dalilin da ya sa wakar mahakar tagulla ta Chambishi ta ke samun farin jini matuka, ba kawai sabo da sautinsa mai dadin sauraro ba ne, har da yadda ta bayyana burin da al’ummar wurin suke son cimmawa game da samun aikin yi da muhallin zama da kyakkyawar makoma. Wakar ta kuma shaida cewa, ingantaccen hadin gwiwa sai da cin gajiyar juna.

A daidai lokacin da muke murnar Ranar Afirka, muna kara yin imanin cewa hadin gwiwar Sin da Afirka bisa manufar rikon gaskiya, kaunar juna da sahihanci, zai ci gaba da rubuta irin labaran yadda Sin da kasashen Afirka ke cin moriyar juna, tare da matse kaimin farfadowar nahiyar Afirka, da kuma taimakawa Sin da Afirka su cimma burin zamanantar da kansu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Chambishi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Chambishi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Sin Na Jinjinawa Kwazon Pakistan Na Shiga Tsakani Domin Maido Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Sin Na Jinjinawa Kwazon Pakistan Na Shiga Tsakani Domin Maido Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.