ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Wakar Mahakar Tagulla Ta Chambishi Ke Samun Farin Jini

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 month ago
Chambishi

Yau ita ce Ranar Afirka, ranar da ke tunawa da samun ’yancin kan al’ummun kasashen Afirka daga mulkin mallaka, wadda kuma ke dauke da burin ’yan Afirka na fita daga talauci da zamanantar da kasashensu. Jama’a, a wannan rana ta musamman, ina so in gabatar muku wata waka da ta yi matukar samun farin jini ta yanar gizo kwanan nan, tare da labarin da ke cikinta. Wakar da ma’aikatan Kamfanin NFCA(Non-Ferrous Company-Africa Mining) da ke Zambiya suka rera ita ce “Wakar Mahakar Tagulla ta Chambishi”. “Down, then up again…” wakar ba kawai ta ba da labarin farfadowar wannan mahakar tagulla mai tsawon tarihi na sama da shekaru 100 ba, har ma ta nuna hadin gwiwa da cin gajiyar juna tsakanin Sin da Afirka.

Turawan Ingila ’yan mulkin mallaka ne suka gano mahakar tagulla ta Chambishi a shekarar 1899, kuma mahakar ta dan bunkasa a hannunsu, amma saboda matsalolin fasaha da gudanarwa, aikin hakar tagulla a wurin ya tsaya cik a shekarun 1980. Daga nan, kamfanonin kasashen yamma suka tafi da ribar da suka ci, suka bar mahakar da ma’aikatanta da rashin aikin yi. A shekarar 1998, kamfanin CNMC(China Nonferrous Metal Mining) ya je wajen mahakar tare da jari, fasaha da kuma zumunta, kuma ya daidaita matsalolin da a baya Turawan suka kasa magancewa tare da farfado da mahakar, har ma ya gina mahakar dijital irinta ta farko a Afirka, inda aka kai ga gudanar da ayyukan hakawa da lodawa da kuma jigila, da injuna da fasahohin kirkirarriyar basira, matakin da ya yi matukar inganta ayyukan ma’aikatan. A lokaci guda, CNMC ya dogara ga mahakar Chambishi wajen fadada masana’antu masu alaka, ciki har da samar da injuna da harhada sinadarai da jigilar kayayyaki da sauransu, inda ya gina yankin masana’antu, baya ga kafa yankin hadin gwiwar tattalin arziki da kasuwanci na Sin da Zambiya, wanda ya jawo kusan kamfanoni 100, don kara inganta tsarin manasana’antu a kasar. A cikin shekaru 20 da suka wuce, kamfanin CNMC ya zuba jarin da yawansa ya kai sama da dala biliyan 1.6 ga mahakar, kuma ya biya harajin dala miliyan 578, baya ga samar da guraben ayyukan yi sama da 6,200. Ban da haka, ya kuma inganta ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya da ci gaban al’ummar garin Chambishi. Abin lura kuma shi ne, a lokacin da yawancin kamfanonin hakar ma’adinai a Zambiya suka dakatar ko rage aikinsu sakamakon matsalar hada-hadar kudi ta duniya da ta kunno kai a shekarar 2008, CNMC ya cika alkawarinsa na “ba za mu rage aikin hakar tagulla ko ton daya ba, kuma ba za mu kori ma’aikaci ko daya ba, kuma ba za mu rage zuba jari ba”, wanda ya tsaya tsayin daka tare da al’ummar wurin don tinkarar kalubalen da suke fuskanta. Don haka tsohon shugaban kasar Zambiya, marigayi Edgar Lungu, ya bayyana CNMC a matsayin “abin koyi ga masu zuba jari na kasashen waje”.

Mahakar Chambishi wani misali ne na hadin gwiwar Sin da Afirka. Da layin dogo na Mombasa zuwa Nairobi a Kenya, da layin dogo mai kwarin daukar nauyi na farko a hamada da ke kasar Aljeriya, da kuma tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Najeriya, kasar Sin ta taimaka wajen gina manyan ayyukan more rayuwa masu yawa a fadin Afirka, wadanda suka inganta hadewa da juna a tsakanin sassan nahiyar da ma sauran sassan duniya, baya ga bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasashen. Har ila yau, daga samar da fasahar noman da ake kira Juncao wajen taimaka wa makiyaya a Mauritania kiwon tumaki, zuwa dakin gwaje-gwajen hadin gwiwa na rigakafin cututtuka da kiwon lafiyar jama’a tsakanin Sin da Tanzaniya, zuwa kawar da gaba dayan harajin fito kan kayayyaki daga kasashen Afirka 53 da ke da huldar diflomasiyya da kasar Sin, hadin gwiwar Sin da Afirka a fannoni daban daban, yana kyautata rayuwar al’ummar kasashe daban daban a Afirka.

ADVERTISEMENT

“Steel in the silence, the town stays alive…Chambishi Copper Mine, Rise again, rise again…”,dalilin da ya sa wakar mahakar tagulla ta Chambishi ta ke samun farin jini matuka, ba kawai sabo da sautinsa mai dadin sauraro ba ne, har da yadda ta bayyana burin da al’ummar wurin suke son cimmawa game da samun aikin yi da muhallin zama da kyakkyawar makoma. Wakar ta kuma shaida cewa, ingantaccen hadin gwiwa sai da cin gajiyar juna.

A daidai lokacin da muke murnar Ranar Afirka, muna kara yin imanin cewa hadin gwiwar Sin da Afirka bisa manufar rikon gaskiya, kaunar juna da sahihanci, zai ci gaba da rubuta irin labaran yadda Sin da kasashen Afirka ke cin moriyar juna, tare da matse kaimin farfadowar nahiyar Afirka, da kuma taimakawa Sin da Afirka su cimma burin zamanantar da kansu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Chambishi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
Chambishi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Sin Na Jinjinawa Kwazon Pakistan Na Shiga Tsakani Domin Maido Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Sin Na Jinjinawa Kwazon Pakistan Na Shiga Tsakani Domin Maido Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Chambishi

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.