ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mugunta Fitsarin Fako…

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Mugunta

Manufar “Amurka ta zamanto Farko” a harkokin zuba jari da gwamnatin Trump ta bullo da ita na ci gaba da yin barazana ga tushen tattalin arzikin Amurkar ita kanta, yayin da tuni saka hannun jari kai-tsaye na kasashen waje (FDI) a Amurkar ya fara ja baya. Dama dai wani rahoto da majalisar hulda da kasashen waje ta kasar ta fitar, ya nuna fargaba a kan lamarin bisa yadda zai haifar da asarar ci gaban tattalin arziki, da samar da ayyukan yi, da sabbin fasahohi.

“Raguwar saka hannun jari wata alama ce da ke nuna cewa manufar ‘Amurka ta zamanto Farko’ tana kange masu zuba jari daga kasashen waje zuwa kasar,” in ji Dokta Mary Lovely, babbar jami’a a Cibiyar Tattalin Arzikin Duniya ta Peterson. Kuma ta kara da cewa, “Idan aka ci gaba da yin hakan, tattalin arzikin Amurka zai tagayyara, kuma sauran kasashe kamar Sin za su cike gurbin da ta bari.”

  • Xi Ya Jaddada Cewa Dole Ne A Dauki Sabbin Nauyi Da Sabbin Ayyuka A Sabuwar Tafiya Ta Inganta Zamanintarwa Irin Ta Kasar Sin
  • Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Naira Miliyan 998 A Cibiyoyin Ciyarwa Na Ramadan

Wani binciken da Cibiyar Kasuwancin Amurka ta gudanar ya gano cewa karin harajin da aka kakaba a karkashin manufar “Amurka ta zamanto Farko” ya haifar da karuwar kashi 15 cikin dari na farashin gudanar da kasuwanci a Amurka idan aka duba mizanin 2024. Inda hakan ya rage gasar kasuwanci a kasar tare da haifar da raguwar fitar da kayayyaki.

ADVERTISEMENT

Shugaban Cibiyar Kasuwancin Amurka, Tom Donohue ya ce, “Karin harajin ya sa kudin fito ya ninka sau biyu a bangaren kasuwancin Amurka. Kuma ba hakan ya kara farashin kaya ba ne kawai, har ma ya kai ga saka haraji na ramakon gayya daga wasu kasashe, tare da rage bukatar kayayyakin da Amurka ke fitarwa.”

Wani bincike da Kungiyar Masu Masana’antu ta Amurka ta gudanar ya gano cewa kashi 80 cikin dari na masana’antun Amurka sun gamu da cikas a bangaren tsarin samar da kayayyakinsu saboda manufar “Amurka ta zamanto Farko”. Kuma hakan yana da mummunan tasiri ga tsadar gudanar da kasuwanci a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Shugaban kungiyar masu masana’antun ta Amurka, Jay Timmons ya ce, manufar ta kasance babban kalubale ga masana’antun kasar, domin ta haifar da rashin tabbas, da wargaza tsara yadda ’yan kasuwa za su tafiyar da kasuwancinsu da kuma saka hannun jari a nan gaba.

Kazalika, wani babban masanin tattalin arziki a Cibiyar Nazarin Tsara Manufofin Tattalin Arziki dake Amurka, Dr. Robert Scott ya ce, manufar ‘Amurka ta Zamanto Farko’ ta kasance bala’i ga ma’aikatan Amurka” domin tana “haifar da asarar aiki, da rage albashi, da rage damammakin ci gaban tattalin arziki ga ma’aikatan Amurka.”

Bayanan wadannan masu ruwa da tsaki sun nuna yadda manufar take shafar Amurkar ciki da waje, kuma dama kasashen duniya musamman kasar Sin sun gargadi kasar cewa, abin ba zai haifar wa hatta ita kanta Amurkar da wani kyakkyawan sakamako ba illa tayar da zaune tsaye.

Bugu da kari, yayin da Amurka ta zabi tafiyar da huldodinta na tattalin arzikin duniya cikin sarkakiya, masu iya magana sun ce, “idan za ka gina ramin mugunta, to gina shi gajere don watakila kai za ka fada”, sannan “Mugunta fitsarin fako, tana komawa ga mai yi!”(Abdulrazaq Yahuza)

Mugunta
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Mugunta
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Gabatowar Azumi

Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Gabatowar Azumi

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.