A daren Lahadin da ta gabata ce, wani mummunan hatsari ya rutsa da wasu matasa kan hanyar su ta zuwa Abuja, matasan sun taso ne tun daga garin Udawa a Jihar Kaduna.
Sun dai gamu da wannan ibtila’in na haɗarin mota ne kan hanyarsu daga Kaduna zuwa Abuja a daidai gadar da za a shiga ƙauyen Jere, lamarin da ya kai ga sun faɗa a ƙarƙashin ita wannan gadar.
Mutane goma ne a cikin motar, amma biyar na asibiti, an samu gawar mutum ɗaya, yayin da sauran mutum huɗu ba a gansu ba a halin yanzu. Ana tsammanin ruwan kogin ya tafi da su ne a daren ranar Lahadi.
Wasu ganau da abin ya faru a gabansu sun shaida wa manema labarai cewa, lamarin ya rutsa da su ne kan hanyarsu ta halartar taron tunawa da halin da iyalan gidan Manzon Allah (SAW) suka shiga a irin wannan watan na Safar, wanda suka yi tattaki na tafiya mai tsawo cikin tsanani da zafin rana daga Karbala zuwa Dimashƙ da ke ƙasar Siriya a yanzu.
Sai dai kawo yanzu ba a samu labarin ganin mutum huɗu daga cikinsu ba.
Hukumar kula da haɗarukan hanya ta ƙasa ta kai sauran asibiti domin ceto rayuwarsu.
A halin yanzu gawar mutum ɗaya tana hannu, yayin da sauran mutum huɗu suna cikin ruwa ba a gan su ba. Daga cikin waɗanda haɗarin ya rutsa da su sun haɗa da, Aliyu Muhammad Udawa da Husaini Nuhu Udawa da Adam Abdullahi Udawa da Abdullahi Mai chaji Udawa da kuma Mubarak Ummar Udawa.
Kawo yanzu, an samu nasarar ciro motar daga ƙasan gadar tare da gawar mutum ɗaya da aka samu.
Kamar yadda ɗan’uwansa ya shaida wa manema labarai cewa sunansa, Aliyu Muhammad daga garin Udawa a Jihar Kaduna, kuma shi ne kawai aka samu gawarsa, sauran huɗu ba agan su ba.














