Ɗan takarar majalisar wakilai a jam’iyyar NDC daga ƙaramar hukumar Dala ta Jihar Kano, Hon. Ali Muhammad Adakawa ya bayyana cewa, zaɓen 2027 idan Allah ya kaimu, mutum za a yi ba jam’iyya ba, musamman mutumin da ke da daraja matuƙar da ya fito neman wani matsayi, zai iya cin zaɓe cikin sauki.
Ɗan takarar majalisar wakilai ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Jihar Kano. Hon. Adakawa ya ce al’ummar Jihar Kano mutane ne masu daraja da mutunci, saboda haka babu maganan a zaɓi APC, canji kawai ake buƙata a jihar a zaɓen 2027 da ma ƙasa baki ɗaya.
A cewarsa, ganin yadda abin da ke faruwa na matsaloli daban-daban, musamman na rashin tsaro da sauransu, wannan zai iya bai wa jam’iyyar NDC samun nasaran cin zaɓe daga ƙasa har sama.
Adakawa ya ce abin da ya fi bai wa muhimmaci a yanzu shi ne, wayar da kai ga al’ummar mazaɓarsa na su fito su karbi katin zaɓe, domin da shi ne mutum zai zaɓi shugaban da yake buƙata, musamman wanda zai kawo masu ci gaba.
Daga ƙarshe, ya gode wa ƙungiyar Gobirawa ta Kwankwaso kan ziyarar da suka kawo masa, inda ya ce mazaɓar da suka fito mazaɓa ce mai matuƙar muhimmanci a siyasar jihar da ma ƙasa baki ɗaya, duk wanda ya ci mazaɓar Gobirawa babu shakka zai iya samun nasara a kowani takara da ya fito.














