ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi Na Nuna Matukar Bukatar Yin Tsayin Daka Wajen Aiwatar Da Matakan Gaggawa

by Sulaiman
5 days ago
Sauyin

Mummunan ibtila’in zabtarewar kasa wanda ya haifar da ambaliyar ruwa da malalar laka a kasar Nepal da kan iyakar jihar Xizang mai cin gashin kai ta Sin, ya kara tunatar da duniya bukatar gaggawa da ake da ita, ta daukar matakan shawo kan matsalar sauyin yanayi wanda ke kara zama babbar barazana ga dorewar rayuwar bil’adama a dukkanin sassan duniyar nan.

Wannan ibtila’i ya sake tunatar da mu cewa, lokaci ya yi da duniya za ta dunkule waje guda domin ceto bil’adama daga halaka.Alkaluman baya bayan nan sun nuna yadda a kasar Nepal, wancan bala’i na malalar laka ya hallaka mutane 1,127, tare da wasu karin mutane 4,800 da suka bace, yayin da a jihar Xizang ta Sin mutane 16 suka rasu, wasu kuma 546 suka bace. Kazalika, akwai wasu daruruwan baki ’yan kasashe da yankuna da dama na duniya da su ma ibtila’in ya rutsa da su.

Kafin wannan bala’i ma, masana da dama sun sha kokawa game da yadda dagawar tudun ruwan teku ke kara barazana ga tsibirai dake kwari, yayin da ake fuskantar karuwar yanayin zafi a wurare da dama ciki har da Turai, yankin da a bana ya fuskanci tsananin zafi, wanda a bazarar bana ya sabbaba mutuwar sama da mutane 30,000.

ADVERTISEMENT

Baya ga haka, sassa da dama na duniya na kara fuskantar yanayin El Niño na dumamar saman teku, wanda hakan ke haifar da karin rashin tabbas, da kara jefa rayukan jama’a cikin hadurra da kuma gurgunta daidaiton zamantakewar al’umma.Yayin da sassan kasa da kasa ke kara azamar bunkasa matakan shawo kan wannan kalubale, kasar Sin a bangarenta, ta himmatu wajen shiga, da bayar da tarin gudunmawa, tana kuma taka rawar gani wajen jagorantar tsarin ayyukan dakile sauyin yanayi a matakin kasa da kasa.

Kasar Sin ta shafe tsawon shekaru tana aiki tukuru a fannin kyautata da kare muhallin halittu, karkashin manufofinta na samar da ci gaba, har ma ta himmatu wajen kaiwa kololuwar fitar da hayakin carbon mai dumama yanayi kafin shekarar 2030, da magance fitar da shi nan zuwa shekarar 2060, da ma sauran manyan matakai da take aiwatarwa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A matakin kasa da kasa kuwa, Sin tana goyon bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar Paris ta sauyin yanayi, da samar da hajoji daga fasahohi marasa gurbata yanayi, irinsu ababen hawa masu aiki da lantarki, da masu aiki da hasken rana da sauransu, wanda hakan ya yi matukar ingiza nasarar matakan shawo kan sauyin yanayi.

Tabbas, ba wani sashe na duniya da zai iya tsira daga matsalolin da sauyin yanayi ke haifarwa. Don haka, wajibi ne dukkanin kasashen duniya su hada karfi da karfe wajen tunkarar wannan kalubale. Wannan lokaci ne da duniya ke matukar bukatar yin aiki tare, ta yadda za a kai ga gudu tare a kuma tsira tare!

Sauyin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Karin Bayani Kan Halartar Shugaban Sin Taron Kolin Sco Na 2026 Da Kuma Ziyarar Aikinsa A Kyrgyzstan Da Masar

Wang Yi Ya Yi Karin Bayani Kan Halartar Shugaban Sin Taron Kolin Sco Na 2026 Da Kuma Ziyarar Aikinsa A Kyrgyzstan Da Masar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.