Gwamnatin Jihar Kwara ta sanar a ranar Laraba cewa mutane 176 da aka yi garkuwa da su yayin harin da aka kai ƙauyukan Woro da Nuku a Ƙaramar Hukumar Kaiama ranar 3 ga Fabrairu, 2026, sun samu ‘yancinsu.
An bayyana hakan ne cikin wani saƙo da gwamnatin jihar ta wallafa a shafinta na Facebook, watanni bayan sace mutanen.
Gwamnatin ta rubuta cewa:”Alhamdulillah, kuma muna yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, hukumomin tsaro da duk waɗanda suka taka rawa wajen samun wannan babbar nasara. Muna matuƙar godiya!”
An yi garkuwa da mutanen ne bayan wasu da ake zargin mayaƙa ne masu alaƙa da ƙungiyar Boko Haram sun mamaye ƙauyukan Woro da Nuku a kan babura, inda suka kai wani tsararren hari da ya ɗauki sa’o’i da dama.
Rahotanni sun bayyana harin a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni da aka taɓa fuskanta a tarihin Jihar Kwara, inda aka ce ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 200, ya jikkata wasu da dama, ya lalata gidaje da kasuwanci, tare da tilastawa mazauna yankin da dama tserewa daga gidajensu.














