ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 583,460 Sun Amfana Da Shirin Hukumar Inshorar Lafiya Ta Jihar Katsina

by Zaharadden Umar
4 weeks ago
Lafiya

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya bayyana cewa an samu ƙaruwar mutane 355,000 da ke amfana da Inshorar lafiya wanda yawan su ya kai 355,000 a shekarar 2023 inda adadin ya kai 583,460 a wannan shekarar kimani kaso 64 a cikin shekaru uku

Raɗɗa ya bayyana haka a ranar juma’a a lokacin da ke ƙaddamar da wasu ƙarin mutane 184,105 cikin shirin Inshorar lafiya da suka haɗa mazaɓo 361 na faɗin jihar Katsina

A cewar sa, sakamakon yana tafiya da kudirin gwamnatin sa na zuba jari da faɗaɗa ingancin kiwon lafiya tare da tabbatar da cewa talaka ya amfana.

ADVERTISEMENT

“Ayau (juma’a) ba wai muna ƙaddamar da shirin ba ne. Muna ƙara ɗaukar wani matsayi ne da zai kai ga samar da ingantaccen kiwon lafiya da al’umma wanda yake damar su ce ba wai alfarma ba, a matsayin na ƴa ƴan jihar Katsina” inji Raɗɗa

Kazalika ya ƙara da cewa jihar Katsina ta zama ɗaya daga jihohin Nijeriya da suke ɗaukar nauyi na aikin kiwon lafiya na Inshora wanda ya samu lambar yabo a shekarun 2024 da 2025

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Haka kuma gwamnan ya bayyana cewa jihohi bakwai sun ziyarci Katsina domin yin koyi da shirin Inshorar lafiya da yadda ake tafiyar da ita a zamanance

Malam Dikko Raɗɗa ya yi bayanin cewa gwamnatin sa ta sake farfarɗo da cibiyoyin kiwon lafiya a faɗin jihar Katsina tare da kafa kayayyakin zamani da suka da katafaren cibiyar ɗaukar hoto da kuma cibiyar duba masu lalurar kansa da gwaje-gwaje tare da ɗaukaka darajar asibitoci da dama.

Sannan gwamna Raɗɗa ya ce kaso 98 na ma’aikatan jiha da ƙananan hukumomi suna cikin wannan shiri na Inshorar lafiya da kuma waɗanda suka ajiye aiki, da mambobin hukumar Hizba da masu muƙata ta musamman kyauta daga gwamnatin jihar Katsina.

Ya kuma yi bayanin cewa shiga wannan shiri na Inshorar lafiya ƙarƙashin gwamnatin jihar Katsina ya zama wajibi ga dukkanin ma’aikatan gwamnati.

Tunda farko da yake jawabi kwamishinan lafiya na jihar Katsina Hon. Musa Adamu Funtua ya ce gwamnatin Dikko Raɗɗa ta farfaɗo da ƙananan asibitoci 200 tare da ɗaukar ma’aikatan lafiya 1,000 tare da faɗaɗa kuɗaɗen magunguna zuwa kaso 400 da kuma ƙara adadin masu amfana da kiwon lafiya kyauta zuwa 207

Lafiya
Zaharadden Umar
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka  Sayawa Iyalinka  Kaji — Imam Nuradden

Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka Sayawa Iyalinka Kaji — Imam Nuradden

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.