Mai taimakawa Gwamnan Jihar Kaduna kan harkokin sadarwa tsakanin gwamnati da talakawa, Imam Nuradden Mujahid, ya bayyana cewa manomi zai iya sayar da takin da gwamnati ta ba shi, ya yi amfani da kudin wajen biyan haya da kuma sayen kaji domin kai wa iyalinsa gida.
Imam Nuradden ya bayyana hakan ne a wata hira da wasu kafafen yada labarai, a sakatariyyar ‘yan jaridu ta jihar Kaduna (NUJ) inda ya ce tallafin takin da gwamnatin Kaduna ke bai wa manoma zai iya rage wa magidanta radadin matsin tattalin arziki da kuma taimakawa wajen inganta zaman aure.
A cewarsa, idan wani magidanci na fuskantar matsala saboda rashin kudi, sayar da takin zai iya ba shi damar samun kudin haya da kuma sayen abinci, wanda hakan zai taimaka wajen kara dankon aure. “Ko da mutum zuwa yayi ya sayar da takin bai kai gona ba kasan takin zai magance matsalar rashin zai sayar da takin ya sayi magani haka zai sayar da takin ya biya kudin makaranta zai kuka magance matsalar kudin haya zai sayar da takin ya biya kudin haya. Akwai wani wanda matarsa bata bashi hadin kai amma yana sayar da takin yaje ya sayi kaji sai kaga tana bashi hadin kai” in ji hi.
Sai dai kalaman nasa sun zo ne yayin da gwamnatin Kaduna ta yi gargadin cewa takin da aka rabawa manoma ba na sayarwa ba ne, kuma duk wanda aka kama yana sayar da shi zai fuskanci hukunci.
Gwamnatin jihar ta raba tireloli 500 na taki ga manoma 150,000 a fadin jihar, a wani yunkuri na rage musu kudin noma da kara samar da abinci.
Imam Nuradden ya kuma yabawa Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, yana cewa manoman jihar Kaduna ba su taba samun gwamnan da ya raba taki mai yawa kamar yadda gwamnatin Uba Sani ta yi ba.
Ya ce tallafin zai rage wa manoma da magidanta radadin tattalin arziki tare da taimakawa wajen bunkasa noma da inganta rayuwar al’umma.














