ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarorin Kasar Sin Manuniya Ce Cewa, Abun Da Hakuri Da Sanin Ya Kamata Bai Kawo Ba, Nuna Karfi Ba Zai Kawo Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Sin

Jiya Talata, cibiyar kimanta darajar tambura a duniya ta Brand Finance mai mazauni a birnin London, ta fitar da wasu rahotanni biyu: daya jeri ne na tambura mafiya karfi da daraja 500 a duniya, yayin da dayan rahoto ne da ya nuna cewa Sin ce kasa daya cikin manyan kasashe 10 da makin manufarta ta jan hankalin kasa da kasa cikin lumana ya karu.

Duk da ana ci gaba da samun sauye-sauye da rashin tabbas a duniya da kuma takkadamar cinikayya da ke ci gaba da kunno kai, kasar Sin na ci gaba da yin zarra da samun tagomashi kusan ta kowane bangare.

Mene ne sirrin kasar Sin?

ADVERTISEMENT

Idan muka dubi rahoto na farko da ya nuna darajar tamburan kasar ta karu a duniya, kana yawansu cikin tambura 500 na duniya ya karu, za mu fahimci cewa wadannan nasarori sun samu ne daga kyawawan manufofin kasar na tallafawa da kare kamfanoninta da kuma ci gaba da bude kofarta da take yi ga kasashen waje. Maimakon nuna wariya da takure kamfanoninta da na ketare, kasar na samar da kyawawan muhalli na kasuwanci da cudanya, da karfafa wa kamfanoninta gwiwar shiga takara da tallafa musu domin tsayawa da kafarsu. Haka kuma manuniya ce cewa, duk wata takkadama ko bita da kulin da ake yi domin ganin faduwarta, sun yi rashin nasara.

Wani dalili shi ne, hangen nesa da kyakkyawan shiri. Misali, tun daga yanzu, cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da za a aiwatar tsakanin 2026 zuwa 2030, kasar Sin ta riga ta yi tanade-tanaden bunkasa sabbin masana’antu ko masana’antu masu tasowa da ma wadanda za su bullo a nan gaba. Wannan yana ba ’yan kasa kwarin gwiwar kirkire-kirkire da habaka kasuwancinsu, saboda sun san cewa, suna da goyon bayan gwamnati, kuma kullum burinta shi ne kare moriyarsu da samar musu damarmakin ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Idan muka kalli rahoto na biyu, za mu fahimce cewa, kasar Sin ba ta shiga sharo ba shanu, ba ta matsin lamba, kuma ba ta neman iko da babakere. Karuwar makin ya nuna kyawawan sakamakon manufofinta na kyautata cudanya tsakaninta da kasa da kasa bisa girmama juna da adalci da taimakekeniya da cin moriyar juna. Ko cikin rahoton, an ambato shirye-shiryenta masu dogon zango kamar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da inganta cudanyar al’adu tsakaninta da kasa da kasa a matsayin misalai. Hakan ya nuna cewa kasa da kasa sun dawo daga rakiyar salon dangantakar kasashen yamma na gindaya sharudda da tsoma baki da babakere, haka kuma abun da hakuri da sanin ya kamata bai kawo ba, tashin hankali da matsi ba zai kawo ba.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
  • Sulaiman
    Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa
  • Sulaiman
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun
  • Sulaiman
    Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

MASU ALAKA

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Next Post
2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

LABARAI MASU NASABA

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.