ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarorin Kasar Sin Manuniya Ce Cewa, Abun Da Hakuri Da Sanin Ya Kamata Bai Kawo Ba, Nuna Karfi Ba Zai Kawo Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

Jiya Talata, cibiyar kimanta darajar tambura a duniya ta Brand Finance mai mazauni a birnin London, ta fitar da wasu rahotanni biyu: daya jeri ne na tambura mafiya karfi da daraja 500 a duniya, yayin da dayan rahoto ne da ya nuna cewa Sin ce kasa daya cikin manyan kasashe 10 da makin manufarta ta jan hankalin kasa da kasa cikin lumana ya karu.

Duk da ana ci gaba da samun sauye-sauye da rashin tabbas a duniya da kuma takkadamar cinikayya da ke ci gaba da kunno kai, kasar Sin na ci gaba da yin zarra da samun tagomashi kusan ta kowane bangare.

Mene ne sirrin kasar Sin?

ADVERTISEMENT

Idan muka dubi rahoto na farko da ya nuna darajar tamburan kasar ta karu a duniya, kana yawansu cikin tambura 500 na duniya ya karu, za mu fahimci cewa wadannan nasarori sun samu ne daga kyawawan manufofin kasar na tallafawa da kare kamfanoninta da kuma ci gaba da bude kofarta da take yi ga kasashen waje. Maimakon nuna wariya da takure kamfanoninta da na ketare, kasar na samar da kyawawan muhalli na kasuwanci da cudanya, da karfafa wa kamfanoninta gwiwar shiga takara da tallafa musu domin tsayawa da kafarsu. Haka kuma manuniya ce cewa, duk wata takkadama ko bita da kulin da ake yi domin ganin faduwarta, sun yi rashin nasara.

Wani dalili shi ne, hangen nesa da kyakkyawan shiri. Misali, tun daga yanzu, cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da za a aiwatar tsakanin 2026 zuwa 2030, kasar Sin ta riga ta yi tanade-tanaden bunkasa sabbin masana’antu ko masana’antu masu tasowa da ma wadanda za su bullo a nan gaba. Wannan yana ba ’yan kasa kwarin gwiwar kirkire-kirkire da habaka kasuwancinsu, saboda sun san cewa, suna da goyon bayan gwamnati, kuma kullum burinta shi ne kare moriyarsu da samar musu damarmakin ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Idan muka kalli rahoto na biyu, za mu fahimce cewa, kasar Sin ba ta shiga sharo ba shanu, ba ta matsin lamba, kuma ba ta neman iko da babakere. Karuwar makin ya nuna kyawawan sakamakon manufofinta na kyautata cudanya tsakaninta da kasa da kasa bisa girmama juna da adalci da taimakekeniya da cin moriyar juna. Ko cikin rahoton, an ambato shirye-shiryenta masu dogon zango kamar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da inganta cudanyar al’adu tsakaninta da kasa da kasa a matsayin misalai. Hakan ya nuna cewa kasa da kasa sun dawo daga rakiyar salon dangantakar kasashen yamma na gindaya sharudda da tsoma baki da babakere, haka kuma abun da hakuri da sanin ya kamata bai kawo ba, tashin hankali da matsi ba zai kawo ba.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

LABARAI MASU NASABA

Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.