ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
5 months ago
APC

Majalisar Matasa ta Jam’iyyar APC wato (APC Youth Parliament) ta yi kakkausar gargaɗi kan jita-jitar da ake ta yaɗawa da ke cewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027, tana bayyana irin waɗannan yunƙurin a matsayin masu hatsari, masu neman janyo rarrabuwar kai, kuma masu iya kawo cikas ga nasarar jam’iyya mai mulki.

 

Kungiyar ta ce ta lura kuma ta damu kan yadda wasu rahotanni ke ƙara yawo a wasu sassan kafafen yaɗa labarai da ke zargin cewa Shugaba Tinubu na tunanin ajiye Shettima tare da maye gurbinsa da wani Kirista ɗan Arewa, wai domin rage sukar tikitin Musulmi da Musulmi da aka yi amfani da shi a zaɓen 2023.

ADVERTISEMENT
  • Darajar Tamburan Kasar Sin Sun Karu A Duniya 
  • AFCON 2025: Lookman Da Osimhen Na Daga Cikin Zaratan Yan Wasa 11 Na Bana

Da ya ke magana da ’yan jarida a Bauchi ranar Litinin, Shugaban Majalisar Matasa ta APC, Kabiru Garba Kobi, ya yi watsi da jita-jitar, yana cewa an ƙirƙire ta ne da gangan domin haddasa rikici a cikin jam’iyyar APC.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

A cewar Kobi, waɗanda ke yaɗa irin waɗannan raɗe-raɗin su na yi ne don muradunsu na ƙashin kai, ba wai don neman haɗin kai da daidaiton jam’iyyar ba.

 

“Duk wani yunƙuri na sauya Sanata Kashim Shettima babban kuskure a siyasance ne da zai iya jawo wa Shugaba Tinubu asarar ƙuri’u mai yawa a Arewa, musamman Arewa-Maso-Gabas,” in ji Kobi.

 

Ya lura cewa masu yaɗa batun na cewa Shugaba Tinubu na duba yiwuwar zaɓan Kirista ɗaya daga cikin tsohon Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara, Ministan Tsaro Laftanar-Janar Christopher Musa (mai ritaya), Gwamnan Jihar Plateau Caleb Mutfwang, da Limamin Katolika na Sokoto, Rabaran Matthew Hassan Kukah domin sauya Shettima da ɗaya daga cikinsu. Kobi ya ce irin waɗannan hasashe kawai da ruɗani da wasu ‘yan siyasa ke haddasawa.

 

Kobi ya amince cewa Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar zaɓar abokin takararsa daga ko’ina a faɗin ƙasar, amma ya jaddada cewa hikimar siyasa, riƙon amana, aminci, da gaskiya su ne ya kamata su jagoranci irin wannan matakin.

 

“Duk abin da ake buƙata daga mataimaki, aminci, sadaukarwa, jarumtaka, gogewar siyasa, da goyon bayan jama’a, Sanata Kashim Shettima na da su ba tare da shakka ba,” in ji shi.

 

Shugaban Majalisar Matasa ta APC ya jaddada cewa Shettima har yanzu shi ne mafi haɗa kan al’umma a Arewa-Maso-Gabas kuma jigo a arewa baki daya da sauran sassan ƙasar nan.

 

“Shettima shi ne mutumin da zai iya tara Arewa ya kawo ƙuri’un da Shugaba Tinubu ke buƙata a 2027. Waɗanda ke kiran a sauya shi, ba wata gudummawar da suka bayar wajen nasarar APC a 2023. Wasu daga cikinsu ma sun yaƙi Tinubu a wancan lokaci, amma yanzu wai su ke neman a sauya wanda ya bada gudunmawa sosai wajen nasarar Tinubu,” in ji Kobi.

 

Ya kuma yi gargaɗi ga Shugaba Tinubu da kada ya saurari masu rura wannan yunƙurin, “Muna roƙon Mai Girma Shugaban Ƙasa kada ya bari a shagaltar da shi da waɗanda ba su taɓa kasancewa ɓangare na gwagwarmayarsa ba. Cigaba da tafiya da Shettima shi ne hanya mafi tabbas ta samun nasara a 2027,” in ji shi.

 

Kobi ya bayyana cewa Majalisar Matasa ta APC ta yi tur da duk wani yunƙuri na janyo cikas ga tikitin Tinubu/Shettima, yana mai cewa ƙarfin jam’iyyar yana tattare da nasara, amincewa, da jagoranci da aka gwada.

 

Da ya ke bayyana Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima a matsayin shugaba mai hangen nesa, kuma mai kishin ƙasa, Kobi ya ce jajircewarsa da salon jagorancinsa na ci gaba da zaburar da matasan Nijeriya.

 

Ya kwatanta tasirin siyasar Shettima a Arewa-Maso-Gabas da na Firayim Ministan Nijeriya na farko, Sir Abubakar Tafawa Balewa, yana cewa matasan yankin na kallonsa a matsayin alamar jarumtaka, sadaukarwa, da haɗin kan ƙasa.

 

Shugaban Majalisar Matasa ta APC ya yi gargaɗi cewa canza matsayin Shettima gabanin 2027 ba wai kawai zai raba jam’iyyar ba ne, har ma zai nisanta miliyoyin masu kaɗa ƙuri’a na Arewa, waɗanda goyon bayansu ke da matuƙar muhimmanci ga nasarar APC a zaɓe.

APC
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Gina Tsarin Cajin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Gina Tsarin Cajin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Mafi Girma A Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.