ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Yunƙurin Sauya Shettima A Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Ɓaraka Zai Janyo A APC – Matasa

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
APC

Majalisar Matasa ta Jam’iyyar APC wato (APC Youth Parliament) ta yi kakkausar gargaɗi kan jita-jitar da ake ta yaɗawa da ke cewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027, tana bayyana irin waɗannan yunƙurin a matsayin masu hatsari, masu neman janyo rarrabuwar kai, kuma masu iya kawo cikas ga nasarar jam’iyya mai mulki.

 

Kungiyar ta ce ta lura kuma ta damu kan yadda wasu rahotanni ke ƙara yawo a wasu sassan kafafen yaɗa labarai da ke zargin cewa Shugaba Tinubu na tunanin ajiye Shettima tare da maye gurbinsa da wani Kirista ɗan Arewa, wai domin rage sukar tikitin Musulmi da Musulmi da aka yi amfani da shi a zaɓen 2023.

ADVERTISEMENT
  • Darajar Tamburan Kasar Sin Sun Karu A Duniya 
  • AFCON 2025: Lookman Da Osimhen Na Daga Cikin Zaratan Yan Wasa 11 Na Bana

Da ya ke magana da ’yan jarida a Bauchi ranar Litinin, Shugaban Majalisar Matasa ta APC, Kabiru Garba Kobi, ya yi watsi da jita-jitar, yana cewa an ƙirƙire ta ne da gangan domin haddasa rikici a cikin jam’iyyar APC.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

A cewar Kobi, waɗanda ke yaɗa irin waɗannan raɗe-raɗin su na yi ne don muradunsu na ƙashin kai, ba wai don neman haɗin kai da daidaiton jam’iyyar ba.

 

“Duk wani yunƙuri na sauya Sanata Kashim Shettima babban kuskure a siyasance ne da zai iya jawo wa Shugaba Tinubu asarar ƙuri’u mai yawa a Arewa, musamman Arewa-Maso-Gabas,” in ji Kobi.

 

Ya lura cewa masu yaɗa batun na cewa Shugaba Tinubu na duba yiwuwar zaɓan Kirista ɗaya daga cikin tsohon Kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara, Ministan Tsaro Laftanar-Janar Christopher Musa (mai ritaya), Gwamnan Jihar Plateau Caleb Mutfwang, da Limamin Katolika na Sokoto, Rabaran Matthew Hassan Kukah domin sauya Shettima da ɗaya daga cikinsu. Kobi ya ce irin waɗannan hasashe kawai da ruɗani da wasu ‘yan siyasa ke haddasawa.

 

Kobi ya amince cewa Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar zaɓar abokin takararsa daga ko’ina a faɗin ƙasar, amma ya jaddada cewa hikimar siyasa, riƙon amana, aminci, da gaskiya su ne ya kamata su jagoranci irin wannan matakin.

 

“Duk abin da ake buƙata daga mataimaki, aminci, sadaukarwa, jarumtaka, gogewar siyasa, da goyon bayan jama’a, Sanata Kashim Shettima na da su ba tare da shakka ba,” in ji shi.

 

Shugaban Majalisar Matasa ta APC ya jaddada cewa Shettima har yanzu shi ne mafi haɗa kan al’umma a Arewa-Maso-Gabas kuma jigo a arewa baki daya da sauran sassan ƙasar nan.

 

“Shettima shi ne mutumin da zai iya tara Arewa ya kawo ƙuri’un da Shugaba Tinubu ke buƙata a 2027. Waɗanda ke kiran a sauya shi, ba wata gudummawar da suka bayar wajen nasarar APC a 2023. Wasu daga cikinsu ma sun yaƙi Tinubu a wancan lokaci, amma yanzu wai su ke neman a sauya wanda ya bada gudunmawa sosai wajen nasarar Tinubu,” in ji Kobi.

 

Ya kuma yi gargaɗi ga Shugaba Tinubu da kada ya saurari masu rura wannan yunƙurin, “Muna roƙon Mai Girma Shugaban Ƙasa kada ya bari a shagaltar da shi da waɗanda ba su taɓa kasancewa ɓangare na gwagwarmayarsa ba. Cigaba da tafiya da Shettima shi ne hanya mafi tabbas ta samun nasara a 2027,” in ji shi.

 

Kobi ya bayyana cewa Majalisar Matasa ta APC ta yi tur da duk wani yunƙuri na janyo cikas ga tikitin Tinubu/Shettima, yana mai cewa ƙarfin jam’iyyar yana tattare da nasara, amincewa, da jagoranci da aka gwada.

 

Da ya ke bayyana Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima a matsayin shugaba mai hangen nesa, kuma mai kishin ƙasa, Kobi ya ce jajircewarsa da salon jagorancinsa na ci gaba da zaburar da matasan Nijeriya.

 

Ya kwatanta tasirin siyasar Shettima a Arewa-Maso-Gabas da na Firayim Ministan Nijeriya na farko, Sir Abubakar Tafawa Balewa, yana cewa matasan yankin na kallonsa a matsayin alamar jarumtaka, sadaukarwa, da haɗin kan ƙasa.

 

Shugaban Majalisar Matasa ta APC ya yi gargaɗi cewa canza matsayin Shettima gabanin 2027 ba wai kawai zai raba jam’iyyar ba ne, har ma zai nisanta miliyoyin masu kaɗa ƙuri’a na Arewa, waɗanda goyon bayansu ke da matuƙar muhimmanci ga nasarar APC a zaɓe.

APC
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
APC
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
APC
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
Sin Ta Gina Tsarin Cajin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Gina Tsarin Cajin Motoci Masu Amfani Da Lantarki Mafi Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
APC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
APC

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
APC

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.