Abokai, nazarin kwayoyin cuta da Amurka take yi a duniya ya dade yana haifar da kalubaloli irin daban-daban. Ciki hadda nazari kan jikin Bil Adama a boye da nazari wasu kwayoyin cuta mafi kamuwa da Bil Adama, har ma da bacewar wasu kwayoyin cuta daga cibiyoyin nazari da sauransu, duk sun kawo babbar illa ga jama’a, inda suka jefa kasashe daban-daban cikin mawuyancin hali na rashin tsaro.
Ran 24 ga watan Fabrairun bara, rikici ya barke tsakanin Rasha da Ukraine, lamarin da kuma ya tona asirin Amurka game da irin wannan nazari da take yi a boye a kasar Ukraine da ma sauran kasashe daban-daban a duniya. Game da wannan batu, kasashe da dama sun nuna shakku da damuwarsu, amma Amurka ta yi kunnen uwar shegu. Har zuwa yanzu, akwai shaiddu dake bayyana cewa, nazarin da Amurka take yi a kasashen waje na fakewa da batun ba da tallafin jiyya ga ketare, na da alaka da ayyukan soja. Wadannan dakunan nazarin da Amurka ta kafa a kasashen duniya, za su kawo babbar illa ga kasashe daban-daban da na al’ummominsu
To, a matsayinta na kasar dake kiran kanta a matsayin “Fitilar da ke haskaka a fannin hakkin Bil Adama”, yaushe ne za ta ba da bayani kan wadannan ayyukan da take yi a sassan duniya?(Mai zana da mai rubuta: MINA)