Jam’iyyar NDC ta nesanta kanta da ’yan takara 10 da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta wallafa a shafinta a matsayin ’yan takarar jam’iyyar a zaben Majalisar Dokokin Jihar Anambra na 2027.
Jam’iyyar ta nace cewa ba ita ta tsayar da mutanen ba, sannan kuma ba ta gabatar da takardunsu na Form EC9E ga hukumar INEC ba.
Haka kuma, NDC ta bukaci a gudanar da binciken na’ura cikin gaggawa kan shafin INEC na karbar bayanan ’yan takara, domin gano yadda sunayen da takardun wadannan mutane suka shiga cikin tsarin hukumar.
Daraktan SKafofin Sadarwa da Tsare-tsaren Sadarwa na NDC, Theophilus Agada, ne ya bayyana matsayar jam’iyyar a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Laraba.
Ya ce, “Sunayen mutane 10 da INEC ta wallafa ba su fito daga tsarin tantancewa da tsayar da ’yan takarar jam’iyyar ba, haka kuma ba su fito daga tsarin daukaka kara na jam’iyyar ba.
“NDC ta tura sunayen ’yan takarar da suka samu nasara a tsarin tantance ‘yan takarar da aka tantance, amma hukumar ta yi watsi da sunayen da jam’iyyar ta amince da su, sannan ta wallafa wasu mutane da ba mu san su ba.”














