Gwamnatin Jihar Kano ta yi alƙawarin bai wa ’yan wasa da jami’an ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars kyautar kuɗi idan suka samu nasara a wasan ƙarshe na kakar bana da za su buga da Plateau United a Jos.
Mai bai wa gwamnan Jihar Kano shawara kan harkokin Matasa da Wasanni, Sani Musa Danja, ne ya bayyana hakan a Kano yayin da ƙungiyar ke ci gaba da shirye-shiryen wasan da za a buga ranar Lahadi a filin wasa na Jos.
A halin yanzu Kano Pillars tana matsayi na 10 a teburin gasar da maki 48, yayin da Plateau United ke matsayi na 12 da maki 47.
Wannan ya sa wasan ya zama mai muhimmanci sosai ga ƙungiyoyin biyu domin kauce wa faɗawa matakin gajiyayyu.
Kano Pillars na buƙatar aƙalla maki ɗaya domin tabbatar da ci gaba da kasancewa a gasar kakar wasa mai zuwa.
Tuni dai ƙungiyoyin Bayelsa United da Wikki Tourists suka faɗi zuwa gasar rukuni na ƙasa bayan sun kammala gasar a matsayi na 19 da na 20.
Sani Danja ya ce kyautar kuɗin za ta ƙara wa ’yan wasan ƙaimi da ƙarfin guiwa domin samun sakamako mai kyau a wasan.
Kano Pillars na daga cikin ƙungiyoyin da suka fi samun nasara a tarihin gasar Nijeriya, inda ta lashe gasar sau huɗu.















Discussion about this post