Kasar Nepal ta matukar godewa kasar Sin bisa tallafin kayan agaji da ta aike mata a lokacin da ta fuskanci ibtilai’in zabtarewar kasa. wannan na kunshe ne cikin jawabin da ministan harkokin wajen Nepal Shisir Khanal ya gabatar, yayin ganawar sa da jakadan Sin a Nepal Zhang Maoming.
Khanal ya ce kasar Sin da Nepal na da alaka wajen tsarin muhallin kasa kuma ibtila’in da aka samu na sauyin yanayi ya shafe su duka, yana mai karawa da cewa kasar Nepal da Sin sun amince cewa magance matsalolin sauyin yanayi, nauyi ne da ya rataya a wuyan al’ummomin duniya.
Ya kuma bayyana cewa kasar Nepal ba ta da aniyar neman diyyar tabbatar da daidaito a fannin batun yanayi daga wata kasa, har da kasar Sin, sai dai kawai za ta nemi diyya ne daga gamayyar kasa da kasa, kamar yadda aka tanada a kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya da kuma yarjejeniyar Paris game da ibitila’in sauyin yanayi.
Ya kuma lura cewa tun lokacin da ibtila’in ya afku, kasar Sin ta tallafa musu ta fuskoki da dama, inda jakadan Sin Zhang ya nuna tabbacin cewa ta hanyar hadin kai da taimakon juna, al’ummomin biyu za su murmure daga wahalhalun da suka fuskanta.
Zhang ya kara da cewa kasar Sin a shirye take ta cigaba da aiki da Nepal da kuma sauran al’ummomin duniya wajen karfafa hadin gwiwa domin karewa da kuma rage tasirin matsalolin sauyin yanayi. (Suleiman Suleiman Ibrahim)














