Mahukuntan Pakistan sun ce hare-haren da Sojin ƙasar suka kai maɓoyar ƴan ta’addan da ke kan iyakarsu da Afghanistan ya kashe mayaƙa 36 tare da jikkata wasu 163, wanda ke matsayin martani ga mummunan harin da aka kai cikin ƙasar a ƙarshen mako.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a Ɗ ministan yaɗa labarai na Pakistan Attaullah Tarar ya ce dukkanin yankuna 3 da sojojin suka kai wa hari a gabashin Afghanistan sun yi nasarar lalata maɓoyar ɓatagarin.
Saƙon na Ataullah na nufin yankunan Afghanistan 3 da suka ƙunshi Paktia da Paktika da kuma Kunar dukkaninsu a yankin gabashin ƙasar da aka kai wa harin tare da kashe mutanen 29 da kuma jikkata wasu da dama baya ga lalata makamansu.
Sanarwar da gwamnatin Taliban a Afghanistan ta fitar ta bakin kakakin gwamnati Hamdullah Fitrat ta ce harin na Pakistan ya kashe fararen hula 36 tare da jikkata wasu 163 waɗanda basu da alaƙa da wata ƙungiya ko kuma kasancewa mayaƙa.
Ma’aikatar harkokin wajen Afghanistan ta ce tuni ta yi sammacin babban jami’in da ke kula da alaƙar ƙasar da Pakistan tare da damƙa masa wasiƙar nuna ɓacin rai kan yadda Islamabad ta saɓa dokokin sararin samaniyar Kabul wajen kai hare-haren yankin gabashi tare da kashe fararen hular da basu ji ba basu gani ba.
Wata sanarwar ma’aikatar harkokin wajen Pakistan ta ce hare-haren lan yankunan 3 martani ne ga harin ranar Asabar a birnin Karachi na kudancin ƙasar da ya kashe Soji guda 3.














