Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya nuna damuwa kan yadda matsalar rashin wadataccen abinci ke ƙara ta’azzara a Arewacin Nijeriya, yana mai cewa lamarin ya zama babban ƙalubale da ke buƙatar matakan gaggawa.
Ya bayyana hakan ne bayan rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) da ya nuna cewa sama da mutum miliyan 17 a jihohi tara na Arewacin Nijeriya na fuskantar matsananciyar yunwa, yayin da fiye da mutum miliyan 35 a faɗin ƙasar ka iya fuskantar ƙarancin abinci a lokacin daminar ƙarancin abinci.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Asabar, Obi ya ce wannan yanayi ya nuna gazawar shugabanci da rashin kyakkyawan tsari, musamman ganin cewa Arewacin Nijeriya ne cibiyar samar da mafi yawan abincin ƙasar.
Ya ƙara da cewa rahotanni sun nuna sama da mutum 10,000 sun shiga matsananciyar yunwa mai barazana ga rayuwa, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da ke neman gaggawar aikin jin ƙai.
Obi ya danganta matsalar da rashin tsaro, yana cewa hare-haren ‘yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya sun hana manoma komawa gonakinsu tare da tarwatsa al’ummomin manoma a jihohi da dama. Ya ce, “Har sai mun tabbatar da tsaron yankunan noma, ba za mu iya tabbatar da makomar ƙasarmu ba. Rashin tsaro ya hana manoma noma, lamarin da ke barazana ga wadatar abinci a Nijeriya.
“Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi su mayar da hankali wajen tabbatar da tsaron yankunan noma tare da bai wa ƙananan manoma isasshen tallafi domin ƙara yawan amfanin gona. Haka kuma ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa da Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) da sauran abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa domin cike giɓin tallafin jin ƙai ga waɗanda rikicin ya shafa.
Rahotannin hukumomin agaji sun nuna cewa rikice-rikice, da ƙauracewa daga muhallai da raguwar tallafin jin ƙai na tura Arewacin Nijeriya zuwa mafi munin matsalar yunwa cikin kusan shekaru goma, inda miliyoyin mutane ke fuskantar matsananciyar rashin wadataccen abinci.













