ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya nuna damuwa kan yadda matsalar rashin wadataccen abinci ke ƙara ta’azzara a Arewacin Nijeriya, yana mai cewa lamarin ya zama babban ƙalubale da ke buƙatar matakan gaggawa.

Ya bayyana hakan ne bayan rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) da ya nuna cewa sama da mutum miliyan 17 a jihohi tara na Arewacin Nijeriya na fuskantar matsananciyar yunwa, yayin da fiye da mutum miliyan 35 a faɗin ƙasar ka iya fuskantar ƙarancin abinci a lokacin daminar ƙarancin abinci.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Asabar, Obi ya ce wannan yanayi ya nuna gazawar shugabanci da rashin kyakkyawan tsari, musamman ganin cewa Arewacin Nijeriya ne cibiyar samar da mafi yawan abincin ƙasar.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa rahotanni sun nuna sama da mutum 10,000 sun shiga matsananciyar yunwa mai barazana ga rayuwa, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da ke neman gaggawar aikin jin ƙai.

Obi ya danganta matsalar da rashin tsaro, yana cewa hare-haren ‘yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya sun hana manoma komawa gonakinsu tare da tarwatsa al’ummomin manoma a jihohi da dama. Ya ce, “Har sai mun tabbatar da tsaron yankunan noma, ba za mu iya tabbatar da makomar ƙasarmu ba. Rashin tsaro ya hana manoma noma, lamarin da ke barazana ga wadatar abinci a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

“Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi su mayar da hankali wajen tabbatar da tsaron yankunan noma tare da bai wa ƙananan manoma isasshen tallafi domin ƙara yawan amfanin gona. Haka kuma ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa da Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) da sauran abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa domin cike giɓin tallafin jin ƙai ga waɗanda rikicin ya shafa.

Rahotannin hukumomin agaji sun nuna cewa rikice-rikice, da ƙauracewa daga muhallai da raguwar tallafin jin ƙai na tura Arewacin Nijeriya zuwa mafi munin matsalar yunwa cikin kusan shekaru goma, inda miliyoyin mutane ke fuskantar matsananciyar rashin wadataccen abinci.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
  • Abubakar Sulaiman
    Ganduje Ya Musanta Jita-jitar Komawa NDC

MASU ALAKA

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.