• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta A Ebonyi Kan Yi Mata Zagon Kasa 

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
PDP Ta Dakatar Da Shugabanta A Ebonyi Kan Yi Mata Zagon Kasa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta dakatar da shugaban jam’iyyar a Jihar Ebonyi, Okorie Tochukwu Okoroafor, bisa zargin yi mata zagon kasa.

Kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na kasa, ya dauki matakin ne a taron gaggawar da ta gudanar a ranar Juma’a, 27 ga watan Janairu, 2023.

  • An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja
  • Dan Gwamnan Jihar Nasarawa Mai Shekaru 36, Hassan Sule Ya Rasu

Ta ce dakatarwar ta zo ne bayan da aka yi nazari sosai kan halin Okoroafor da kuma ayyukansa a matsayinsa na shugaban jam’iyyar na Jihar Ebonyi.

Dakatarwar ta zo ne sa’o’i 24 bayan jam’iyyar PDP ta gudanar da yakin neman zabenta na shugaban kasa a jihar.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa, Hon. Debo Ologunagba, ya ce “Duba da sashe na 29 (2) (b) da 57 (3) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar PDP, ta amince da dakatarwar a madadin kwamitin zartarwa na kasa ya yi wa Okorie Tochukwu Okoroafor daga yau Juma’a 27 ga watan Junairu, 2023, kan zargin yin zagon kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

“Saboda haka, Okoroafor an mika shi ga kwamitin ladabtarwa na jam’iyya don ci gaba da daukar mataki.”

Dakatar da Okoroafor ya biyo bayan dakatar da ‘yan jam’iyyar da aka yi a baya-bayan nan saboda wasu ayyukan da suka saba wa jam’iyyar.

A makon da ya gabata ne jam’iyyar ta dakatar da Sanata Chimaroke Nnamani da kuma wasu jiga-jigan jam’iyyar na Jihar Ekiti kan kin shiga sabgogin jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EbonyiPDPShugaban Jam'iyyaZagon Kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

Next Post

Ana Tuhumar Mutum 8 Da Aikata Luwadi Da Fashi A Zamfara

Related

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

3 hours ago
Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani
Manyan Labarai

Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

5 hours ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata

7 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina

7 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano

8 hours ago
Next Post
Ana Tuhumar Mutum 8 Da Aikata Luwadi Da Fashi A Zamfara

Ana Tuhumar Mutum 8 Da Aikata Luwadi Da Fashi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

July 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

July 14, 2025
Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

Za A Yi Taron Shugabannin Matasa Na Farko Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka A Nanjing

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.