Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wani yaro ɗan shekara 10 a gidansu da ke ƙaramar hukumar Tarmuwa a Jihar Yobe, kuma suna neman kuɗin fansa domin su sake shi.
A cewar masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, lamarin ya faru da misalin ƙarfe 5:20 na yammacin ranar 25 ga watan Yuli a ƙauyen Andarashi.
Rahotanni sun ce wasu mutane huɗu ɗauke da makamai sun kutsa gidan Bukar Umar tare da sace yaron mai suna Abdullahi Isa.
An ce maharan na ɗauke da baka da kibiyoyi, adda da kuma sanduna. Bayan sun sace yaron, sun tsere zuwa wani waje da ba a sani ba.
Daga baya, waɗanda suka sace yaron sun kira iyayensa ta waya, inda suka buƙaci a biya kuɗin fansa kafin su sake shi.
Rundunar ‘yansandan ta tura jami’anta zuwa yankin tare da fara bincike. Haka kuma, Sashen Binciken Manyan Laifuka na jihar (SID) ya fara bibiyar lambar wayar da ake zargin masu garkuwar suka yi amfani da ita.
‘Yansanda sun ce suna ci gaba da ƙoƙarin ceto yaron cikin ƙoshin lafiya tare da cafke waɗanda suka aikata wannan laifi.














