Dubban magoya bayan jam’iyyarADC) sun fice daga jam’iyyar tare da komawa APC a Garin Gorau da ke ƙaramar hukumar Goronyo a Jihar Sakkwato.
Sauya sheƙar ta faru ne a yankin da Hon. Bashir Usman Gorau, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Gada/Goronyo, yake da ƙarfin siyasa.
Ana kallon lamarin a matsayin babban koma baya ga ADC a Yankin Sanatan Sakkwato ta Gabas.
An tarbi sabbin mambobin ne a wani taro da shugabannin APC da magoya bayanta suka halarta.
Mataimakin Shugaban APC na Shiyyar Sakkwato ta Gabas, Alhaji Muhammad Musa Sarkin Alaru, ya yi musu maraba tare da tabbatar musu da cewa za su samu dama iri ɗaya da sauran mambobin jam’iyyar.
Da yake jawabi a wajen taron, Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan jihar Ahmad Aliyu, Alhaji Hussaini N. Umar Gorau, ya ce yawaitar sauya sheƙar da ake gani a jihar na da nasaba da ayyukan gwamnatin jihar a fannonin gina hanyoyi, bunƙasa karkara, noma da kuma inganta tsaro.
Shi ma Shugaban APC na ƙaramar hukumar Goronyo, Alhaji Sa’idu Muhammad Goronyo, ya buƙaci sabbin mambobin su kasance masu biyayya da haɗin kai domin ƙara ƙarfafa jam’iyyar.
A madadin waɗanda suka sauya sheƙar, Nasiru Mukhtar Gorau, ya ce sun shiga APC ne saboda ayyukan ci gaba da gwamnatin Gwamna Ahmad Aliyu ta gudanar, musamman wajen gina ababen more rayuwa da inganta tsaro.
An kuma karrama Ƙaramin Ministan Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, da Alhaji Hussaini N. Umar Gorau, da kuma ɗan takarar Sanatan APC na Sakkwato ta Gabas, Alhaji Umar Ajiya, saboda gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban al’umma da kuma bunƙasa jam’iyyar.














