ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Magoya Bayan ADC Sun Sauya Sheƙa Zuwa APC A Sakkwato

by Sadiq
2 hours ago

Dubban magoya bayan jam’iyyarADC) sun fice daga jam’iyyar tare da komawa APC a Garin Gorau da ke ƙaramar hukumar Goronyo a Jihar Sakkwato.

Sauya sheƙar ta faru ne a yankin da Hon. Bashir Usman Gorau, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Gada/Goronyo, yake da ƙarfin siyasa.

Ana kallon lamarin a matsayin babban koma baya ga ADC a Yankin Sanatan Sakkwato ta Gabas.

ADVERTISEMENT

An tarbi sabbin mambobin ne a wani taro da shugabannin APC da magoya bayanta suka halarta.

Mataimakin Shugaban APC na Shiyyar Sakkwato ta Gabas, Alhaji Muhammad Musa Sarkin Alaru, ya yi musu maraba tare da tabbatar musu da cewa za su samu dama iri ɗaya da sauran mambobin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Da yake jawabi a wajen taron, Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan jihar Ahmad Aliyu, Alhaji Hussaini N. Umar Gorau, ya ce yawaitar sauya sheƙar da ake gani a jihar na da nasaba da ayyukan gwamnatin jihar a fannonin gina hanyoyi, bunƙasa karkara, noma da kuma inganta tsaro.

Shi ma Shugaban APC na ƙaramar hukumar Goronyo, Alhaji Sa’idu Muhammad Goronyo, ya buƙaci sabbin mambobin su kasance masu biyayya da haɗin kai domin ƙara ƙarfafa jam’iyyar.

A madadin waɗanda suka sauya sheƙar, Nasiru Mukhtar Gorau, ya ce sun shiga APC ne saboda ayyukan ci gaba da gwamnatin Gwamna Ahmad Aliyu ta gudanar, musamman wajen gina ababen more rayuwa da inganta tsaro.

An kuma karrama Ƙaramin Ministan Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, da Alhaji Hussaini N. Umar Gorau, da kuma ɗan takarar Sanatan APC na Sakkwato ta Gabas, Alhaji Umar Ajiya, saboda gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban al’umma da kuma bunƙasa jam’iyyar.

MASU ALAKA

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole
Manyan Labarai

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

July 28, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Next Post
Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba - Oshiomhole

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

July 28, 2026
Dubban Magoya Bayan ADC Sun Sauya Sheƙa Zuwa APC A Sakkwato

Dubban Magoya Bayan ADC Sun Sauya Sheƙa Zuwa APC A Sakkwato

July 28, 2026
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Laftanar Din Soja A Yobe

‘Yan Bindiga Sun Sace Yaro Ɗan Shekara 10 A Yobe, Sun Nemi Kuɗin Fansa

July 28, 2026

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.