Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta ba da umarnin kulle dukkan gidajen nishaɗi a faɗin jihar nan take, ciki har da cibiyoyin taruka (gidajen gala) da kuma wuraren DJ.p
Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya bayar da umarnin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.
ADVERTISEMENT
“Tun daga ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, duk irin waɗannan wuraren (cibiyoyin nishaɗi) za su ci gaba da kasancewa a rufe har zuwa ƙarshen watan Ramadan mai tsarki.
“Umarnin zai fara aiki daga ƙarfe 10:00 na dare a wannan rana (yau, Laraba,” in ji sanarwar.















Discussion about this post