Dan takarar kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya a zaben 2027 mai zuwa, Ambasada Yerima Usman Shettima, ya bayyana cewa ba zai bai wa jam’iyyar APC da al’ummar mazabar kunya ba idan aka ba shi dama ya wakilce su a Majalisar Dattawa.
Shettima ya bayyana hakan ne yayin da ya kai ziyara sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar Kaduna, inda ya gabatar da kansa a hukumance a matsayin dan takarar kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya.
“Ya ce idan ya samu nasara a zaben, zai yi wa’adi guda daya ne kacal na shekaru hudu, domin bai wa gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, damar dawowa kan kujerar a nan gaba”.
Dan takarar ya yaba da irin ayyukan ci gaba da gwamnan Uba Sani ke gudanarwa a fadin jihar, yana mai cewa an samu gagarumin sauyi a karkashin jagorancinsa, musamman wajen inganta rayuwar al’umma a birane da karkara.
“Ni dan gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiyya ne. Ni da Gwamna Uba Sani da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, duk a wannan tafiya muka hadu. Saboda haka za mu ci gaba da mara musu baya domin ganin sun samu nasara a zabe mai zuwa,” in ji Shettima.
A nasa bangaren, Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kaduna, Atiku Sanke, ya bayyana cewa kofar jam’iyyar a bude take ga duk masu sha’awar tsayawa takara, domin tabbatar da hadin kai da nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa.
Sanke, wanda sakataren jam’iyyar, Abubakar Rabiu Abubakar, ya wakilta, ya ce babu shakka Yerima Shettima jajirtaccen dan gwagwarmaya ne wanda jam’iyyar ke alfahari da shi.
Ya kara da cewa jam’iyyar APC ta samu gagarumar nasara a karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, musamman wajen samar da ayyukan more rayuwa da bunkasa ci gaban jihar Kaduna baki daya.















Discussion about this post