Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya al’ummar Hausawa da ke Nijeriya, Afirka da sauran sassan duniya murnar Ranar Hausa ta Duniya ta 2026, yana mai bayyana harshen Hausa da al’adun Hausawa a matsayin muhimman ginshikan asalin Afirka, hadin kai da ci gaba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Laraba.
Gwamna Yusuf ya ce bikin na shekarar 2026, mai taken “Al’adarmu, Makomarmu”, ya samar da wata muhimmiyar dama ga Hausawa da sauran al’ummar Afirka wajen yin tunani kan bukatar kare harshensu, al’adunsu, tarihinsu da kuma dabi’un gargajiya domin isar da su ga al’ummomin da za su zo nan gaba.
Gwamna Yusuf ya bayyana cewa, “Ranar Hausa ta Duniya, wadda dan jarida Abdulbaki Jari ya fara a shekarar 2015 tare da hadin gwiwar abokan aikinsa na kafafen sada zumunta, ta bunkasa zuwa wani dandali na duniya wajen inganta harshen Hausa da kuma nuna dimbin al’adun Hausawa masu tarihi”.
Ya yabawa wadanda suka shirya bikin bisa zabar Daura, wadda ake daukarta a matsayin tushen wayewar daular Hausawa, a matsayin cibiyar gudanar da bikin na bana.
Gwamnan ya ce bikin zai kunshi gagarumin bukukuwa a hawan Dawakai mai kayatarwa, wadda za ta baje kolin arzikin al’adun Hausawa, tarihinsu da kuma kyawawan dabi’un gargajiyarsu.














