Masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar ADC a Kudancin Jihar Kaduna sun bukaci Isa Ashiru Kudan, da ya dakatar da naɗin Barista Emmanuel Kantyok a matsayin mataimakin ɗan takararsa na gwamna a zaɓen 2027, har sai Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NWC) ya yanke hukunci kan rikicin tikitin takarar gwamna na jam’iyyar.
Sun bayyana wannan buƙata ne yayin wani taron manema labarai da suka gudanar a Kafanchan, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, inda suka yi gargadin cewa naɗa mataimakin ɗan takara kafin warware rikicin tikitin gwamna na iya ƙara rura wutar rabuwar kai a cikin jam’iyyar gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Da yake jawabi a madadin ƙungiyar, mai gudanar da ita, Solomon Chindo, ya ce cece-ku-cen da ya biyo bayan sakamakon zaɓen fidda gwani na gwamna na ADC ya haifar da ruɗani, don haka ya kamata shugabannin jam’iyyar na ƙasa su fara warware rikicin kafin a ɗauki wani sabon matakin siyasa.
Chindo ya ce dakatar da naɗin mataimakin ɗan takara har sai NWC ta tantance wanda shi ne sahihin ɗan takarar gwamna zai taimaka wajen tabbatar da adalci, ƙarfafa dimokuraɗiyyar cikin gida da kuma inganta haɗin kai a cikin jam’iyyar.
A cewarsa, ci gaba da naɗin mataimakin ɗan takara kafin a warware rikicin na iya ƙara ta’azzara matsalar tare da kawo cikas ga ƙoƙarin haɗa kan jam’iyyar domin tunkarar zaɓen shekarar 2027.














