ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Harin ‘Yan Bindiga Ya Ci Rayukan Mutane 22 A Sokoto

by Sulaiman
3 weeks ago
Sokoto

Aƙalla mutane 22, ciki har da Babban Limamin Masallacin Jumu’a na Izala dake Ungushi, Imam Aliyu, ne aka kashe a wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa al’ummar Ungushi, da ke Ƙaramar Hukumar Kebbe ta Jihar Sokoto.

Rahotanni sun ce an kashe mutanen ne yayin harin da maharan suka kai wa al’ummar garin a yammacin ranar Lahadi, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin fargaba tare da ƙara haifar da damuwa kan taɓarɓarewar tsaro a yankin.

Majiyoyi daga al’ummar garin sun ce maharan sun shiga Ungushi tare da buɗe wa mazauna garin wuta, inda suka kashe mutane da dama, ciki har da malamin addinin Musulunci.Wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce sabon harin ya jefa al’ummar cikin tsananin baƙin ciki da ruɗani.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin ya yi kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su gaggauta ƙara yawan jami’an tsaro a Ungushi da sauran ƙauyukan da ke makwabtaka da ita.

Wannan sabon harin ya zo ne a daidai lokacin da ake samun ƙarin barazanar tsaro a Ƙaramar Hukumar Kebbe, inda rahotanni suka ce wasu al’ummomi da dama sun fuskanci hare-haren ‘yan bindiga, satar dabbobi da kuma raba mutane da muhallansu a cikin ‘yan makonnin nan.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Majiyoyin yankin sun kuma ce wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da shanu sama da 300 da rakuma bakwai daga Ungushi da ƙauyen Gwandi da ke makwabtaka da ita, yayin da wasu mazauna garuruwan suka tsere saboda tsoron hare-hare.

Wannan lamari ya faru ne kwanaki kaɗan bayan rahotannin wani babban hari da ake zargin mambobin ƙungiyar ta’addanci ta Lakurawa ne suka kai a wasu sassan Kebbe.

Rundunar ‘Yansndan Jihar Sokoto ta tabbatar da faruwar lamarin a yankin, amma ta ce tana ci gaba da tattara bayanai kafin fitar da cikakken bayani.

Ƙarin taɓarɓarewar tsaro a yankin ta sanya rundunar soji ƙara mayar da hankali kan Ƙaramar Hukumar Kebbe, inda Babban Kwamandan Runduna ta 8 ta Sojojin Nijeriya, Manjo Janar Bemgba Paul Koughna, ya ziyarci Sansanin Soji na Gaba-gaba (FOB) Kebbe ranar Lahadi domin duba halin tsaro da kuma shirye-shiryen dakarun domin yaki da sabbin barazanar da aka samu.

An ce ziyarar ta mayar da hankali ne kan tantance halin tsaro a zahiri da kuma ƙarfafa martanin sojoji ga barazanar da ƙungiyoyin ‘yan ta’adda da ke aiki a yankin ke haifarwa.

Sokoto
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Manufar Soke Haraji Ta Sin: Kyakkyawan Misali Da Ke Adawa Da Kariyar Cinikayya

Manufar Soke Haraji Ta Sin: Kyakkyawan Misali Da Ke Adawa Da Kariyar Cinikayya

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.