• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sai An Sha Wuya A kan Sha Dadi

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sai An Sha Wuya A kan Sha Dadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa, duk kasar dake fatan samun ci gaba har ma a rika jin amonta a duniya, wajibi ne al’ummarta su zage damtse wajen ganin wannan buri ya tabbata.

Kamar sauran al’ummomin kasashen duniya, al’ummar Sinawa sun hada karfi da karfe wajen gina kasar Sin mai bin tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin a sabon zamani.

  • Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Gagarumin ci gaban da kasar Sin ta cimma a cikin shekaru 10 da suka gabata (2012-2022), sun hada da fannonin tattalin arziki, da binciken sararin samaniya, da fannin kirkire-kirkire da inganta muhalli da zaman rayuwar jama’a da sauransu.

Bayanai na cewa, karfin tattalin arzikin kasar Sin ya kai wani sabon matsayi, ma’aunin GDPn kasar ya kai Yuan triliyan 114, adadin da ya kai kashi 18 bisa dari na karfin tattalin arzikin duniya, wanda bai wuce kashi 11.4 bisa dari ba a shekarar 2012. Masu iya magana na cewa, idan ka ga wane ba banza ba.

A wadannan shekaru, kasar Sin ta ba da gudummawar kashi 30 bisa dari ta fuskar bunkasuwar tattalin arzikin duniya, wadda ta kasance babbar kasar dake taimakawa karuwar tattalin arzikin duniya. Kana ta yi nasarar warware babbar matsalar fama da kangin talauci, wadda ta damu jama’ar Sin cikin dubban shekaru a baya.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Yanzu haka, akwai mazauna kauyuka kimanin miliyan 98.99 da suka yi ban kwana da kangin talauci. Adadin kauyukan da suka sauya zuwa birane, ya karu daga 53.1% zuwa 64.7%. Mazauna kauyuka kimanin miliyan 180 sun kaura zuwa birane.

A matsayinta na kasar dake kan gaba wajen yawan masu amfani da intanet a fadin duniya, kuma daya daga cikin bangaren da kasar ta samu gagarumin nasara, kasar Sin na kan hanyar sauyawa daga yawan adadi zuwa raya harkar intanet mai inganci, da gina tsarin tafiyar da yanar gizo mai cike da tsaro, sakamakon kyautatuwar ababen more rayuwa masu inganci, da ci gaban fasaha da bunkasar tattalin arziki na zamani. Hakika kasar Sin ta ciri Tuta.

Tsakanin wadannan shekaru da muke batu, adadin masu amfani da yanar gizo a kasar Sin, ya karu daga miliyan 564 zuwa fiye da biliyan 1.03, abin da ya sanya ta zama matsayi na daya a duniya. Kasar Sin ta samar da manyan hanyoyin sadarwa na 5G da layin fiber optic mafi girma a duniya. Kuma duniya ta shaida wannan nasara.

Darajar tattalin arzikin zamani na kasar Sin, ta tashi daga kudin Sin RMB yuan tiriliyan 11 kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 1.6 a shekarar 2012 zuwa yuan tiriliyan 45.5 a shekarar 2021, wanda ya sanya ta ci gaba da zama kasa ta biyu a duniya a cikin shekaru da dama a jere.

Yawan jimillar tattalin arzikin zamani a GDPn kasar, shi ma ya karu daga kashi 21.6 cikin 100 a shekarar 2012 zuwa kashi 39.8 cikin 100 a shekarar 2021.

Hada-hadar cinikayyar Intanet ta kasar Sin da tsarin biyan kudi ta wayar salula, duk sun kasance a kan gaba a duniya.

Nasarorin da kasar Sin ta cimma a fannoni daban-daban, a wadannan shekarun da suka gabata, ba nasara ce kawai ga kasar Sin kadai ba, nasara ce ga duniya baki daya.

Hakan ya kara jaddada cewa, sai an zubar da ruwa a kasa kafin a taka damshi. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yajin Aiki Zai Ci Gaba Tun Da Gwamnati Ta Kasa Dauki Matakin Da Ya Dace – ASUU

Next Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Alluran Rigakafin COVID-19 Ta Haifar Da Kyakkyawan Sakamako

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

2 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

3 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

4 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

5 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

6 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

16 hours ago
Next Post
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Alluran Rigakafin COVID-19 Ta Haifar Da Kyakkyawan Sakamako

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Alluran Rigakafin COVID-19 Ta Haifar Da Kyakkyawan Sakamako

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.