Gwamnatin Jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na gina kananan madatsun ruwa domin ba da damar noma a duk tsawon shekara tare da kara yawan samar da abinci.
Kwamishinan Aikin Gona na jihar, Umar Tanko Tunga, ne ya bayyana hakan jiya yayin wani taron bayani na ma’aikatun gwamnati da Ma’aikatar Yada Labarai, Al’adu da Yawon Bude Ido ta jihar ta shirya tare da hadin gwiwar Majalisar Kungiyar ’Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) reshen Nasarawa a Lafia.
Ya ce za a gina wadannan kananan madatsun ruwa a wurare da aka tanada domin tallafa wa noman ban ruwa.
Tunga ya bayyana cewa wannan shiri ba kawai zai kara yawan samar da abinci ba ne, har ma zai samar da ayyukan yi ga matasa da mata ta hanya mai amfani.
Ya kara da cewa tun da farko Gwamnatin Tarayya ta amince da gina manyan madatsun ruwa guda biyu a Lafia da Tide, tare da kammala aikin Farin Ruwa domin samar da wutar lantarki ta ruwa, noman ban ruwa da kuma samar da ruwan sha. A cewarsa, kananan madatsun ruwan da jihar ke shirin ginawa za su kara karfafa kokarin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da wadatar abinci.
Kwamishinan ya jaddada cewa gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule ta samu manyan nasarori a fannin noma, inda ta jawo dimbin jarin masu zuba jari na cikin gida da na kasashen waje.
Ya bayyana gonar shinkafa ta Jangwa/Agwatashi mai fadin hekta 10,000 a matsayin mafi girman hadin gwiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu a fannin noma a yankin Arewa ta Tsakiya.
A cewarsa, wannan shiri ya bai wa mata da matasa da dama damar samun ci gaba a darajar noman shinkafa tare da kara musu kwarewa a noman zamani da amfani da injuna.
Tunga ya kuma bayyana cewa manufar gwamnatin jihar ta kasance mai jan hankalin masu zuba jari, lamarin da ya samar da kafa Katafariyar Cibiyar Masana’antar Sarrafa Rogo (SCIC) mai fadin hekta 10,000 ta kamfanin Sekuoia Holdings Ltd a Karamar Hukumar Kokona.














Discussion about this post