ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkakkiyar Zargin Da Gwamnatin Abba Ke Wa Ganduje

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Ganduje

Tun bayan da Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya karbi rantsuwar kama aiki, ya yi alkawarin bincikar tsohon gwamnan Kano kuma shugaban  Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje kan zargin almundahana, karbar cin hancin dala da kuma zargin da ake masa na kasafta wasu wurare mallakar al’ummar Jihar Kano ne.

Wannan tasa kwana kadan da karbar ranatsuwar Gwamna Abba ya fara dirar wa wasu gine-gine a filin idi da kuma kantunan da aka gina a filin sukuwa, sannan kuma ta dirar wa ginin tsohon otal din Daula.

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
  • Za A Fara Amfani Da Sabon Layin Jirgin Ƙasa Na Dakon Kaya Daga Legas Zuwa Kano A Watan Gobe

Daukar wannan mataki ya sa ‘yan kasuwar filin wadanda aka rushe wa kantunansu suka garzaya gaban kotu, inda ita kuma kotun ta dakatar da gwamnatin Kano daga ci gaba da aiwatar da wannan rusau tare da tarar naira biliyon uku. Wannan mataki na kotu ne ya dakatar da yunkurin Gwamnatin Abba na ci gaba da rushe ire-iren wadanna wurare.

ADVERTISEMENT

Tun daga lokacin da Jam’iyyar NNPP mai mulkin Kano ta kai bantenta a kotun koli, sai labari ya sauya, inda aka fara karkade tsoffin zarge-zargen da ake yi wa tsohon Gwamna Ganuje, wanda suka hada da karbar dala, watandar filayen mallakar gwamnatin Jihar Kano da wasu laifuka da ake zargin shugaban Jam’iyyar APC na kasa ya aikata.

Gwamnatin Kano ta himmatu wajen cika alkawarin da ta yi wa Kanawa na bincikar Ganduje, wanda tun da farko an ji cewa dansa ya gurfanar da mahaifiyarsa, Farfesa Hafsat Ganduje a gaban kotu kan zargin wawure kudaden wasu ‘yan kwankgila. Wannan tasa cikin kunshin zargin da Gwamnatin Abba ke yi wa Ganduje har da batun iyalansa, wanda aka gwamnatin Kano ta kaddamar da kwamtin bincike guda biyu a kansa.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A lokacin kaddamar da kwamitin binciken, Gwamna Abba ya bukaci su tabbatar an hukunta wanda duk aka samu da laifi. A cikin wani jawabi da mai magana da yawun Gwamnatin Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ya bayyana cewa, gwamnan ya jadddada aniyarsa na bincikar al’mundahanar dukiyar al’ummar Kano, wanda hakan na cikin kokarinsa na zakulowa tare da hukunta duk wanda ke da hannu cikin yunkurin tayar da tarzoma a Jihar Knao.

Kwamitin farko na karkashin Mai Shari’a Zuwaira Yusuf, wadda aka dora wa alhakin bincikar rikicin siyasar tare da batan mutane daga shekara ta 2015 zuwa 2023, sai kuma kwamiti na biyu da ke karkashin jagorancin Mai Shari’a Faruk Lawan wanda aka dora wa alhakin bincikar almundahanar kadarorin al’umma.

Kamar yadda aka tabbatar alkalan na da kyakkyawan tarihin ingancin aiki da kuma gaskiya da adalci, wanda hakan a dukkan zaton da ake za a iya samun adalci cikin aikin biciken. An dai bai wa kwamitocin binciken wa’adin watanni uku domin gabatar da rahotonsu.

Gabanin kaddamar da wadannan kwamitocin bincike, an ta samun musayar zafafan kalamai tsakanin Ganduje da kuma Gwamna Abba, wanda tun da farko Ganduje ya zargi Gwamnatin Kano da kulla kitimurmurar haddasa zanga-zangar bukatar sai ya sauka daga shugabancin jam’iyyar APC, haka kuma ya zargi Gwamnatin Kano da kulla wani shirin korarsa daga mazabarsa, wanda ya ce duk wannan ba zai sa ya jijjiga ba wajen ci gaban ayyukan alhairin da yake yi.

 Anasa bangaren, Gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabri Yusuf ya musanta wannan zargi ta bakin mai magnaa da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa wanda ya ce, kamata ya yi Ganduje ya shagala da abin kunyar da ya tafka tare da shirya fuskantar binciken da ake masa, ba wai ya shagala da kazafin gazawar gwamnati mai ci a yanzu ba. Sanusi ya shaida cewa Gwamnatin Abba ba za ta bari batun dala ya lalace ba, saboda haka suka bukaci hukumar EFCC da ta fito da sakamakon binciken faifan dala da suka gudanar domin jama’a su san halin da ake ciki.

A wata sabuwa kuma, dan Ganduje wanda tun da farko ya fara gurfanar da mahaifiyarsa gaban kotu kan korafin wasu kudade, an hange shi ya ziyarci ofishin shugaban hukumar karbar korafe-korafe ta Jihar Kano. Ya tabbatar wa da shugaban hukuma Muhuyi Magaji Rimin Gado cewa zai taimaka wa hukumar wajen ba da shaida domin samun nasarar bincikar mahaifin nasa.

A zaman kotun da aka a ranar Litinin ta makon jiya, wanda aka gudanar a kotu mai lamba ta uku da ke zamanta a sakatariyar Audu Bako a Kano, alkalin kotun ya bukaci dukkan bangarorin guda biyu su shirya gabatar da bayanansu a zaman da za a yi nan ga ba kadan.

Ganduje na cikin tsaka mai wuya, kasancewar ana ta gudanar da zanga-zangar neman sauke shi daga mukamin shugaban jam’iyyar APC na kasa, yayin da a hannu guda kuma yake fuskanta matukar adawar cikin gida, inda wasu  ke zargin faduwar jam’iyyar a kotun koli da hadin bakisa domin biyan wata bukata, sai dai kuma yadda Gwmanatin Kano ke yin duk mai yiwuwa domin ganin an gurfanar da Ganduje tare da wasu daga cikin iyalansa saboda su fuskanta hukuncin abin da suka aikata.

A yanzu haka an fara ganin wata sabuwar hula wadda ke dauke da kalar ja da samfurin hular Tinubu, wadda hakan ke nuna alama cewa kila ana kan shirye-shiryen sauya shekar Jam’iyya NNPP zuwa APC, wannan kuma na cike da manyan kalubale, musamman tsoron da Kwankwasa ke yi na komawa APC karkashin Ganduje, idan haka ta faru kenan har yanzu Kwankwaso da Kwankwasiyya na karkashin Ganduje.

Wani hange da ake yi wa Shugaba Tinubu cewar sai dai ya zabi guda cikin wadannan manyan ‘yan siyasar Kano, ma’ana ko dai ya hakura da Gnaduje ya karbi Kwankwaso, ko kuma ya bar Kwankwaso ya kama Ganduje, wanda kuma yin hakan shi ma a gareshi babban kalubale ne ga zaben 2027.

Ganduje
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sin Ta Goyi Bayan Kudurin Kwamitin Tsaron MDD Na Sake Gaggauta Duba Yiwuwar Amincewa Da Bukatar Falasdinu Ta Zama Mamba A MDD

Sin Ta Goyi Bayan Kudurin Kwamitin Tsaron MDD Na Sake Gaggauta Duba Yiwuwar Amincewa Da Bukatar Falasdinu Ta Zama Mamba A MDD

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.