ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
SDP

Kwamitin gudanarwa na ƙasa (NWC) na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ya sanar da korar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, daga jam’iyyar, tare da hana shi duk wata hulɗa da jam’iyyar na tsawon shekaru 30 masu zuwa.

A cewar kakakin jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Rufus Araba Aiyenigba, an ɗauki matakin ne bayan gudanar da bincike mai zurfi dangane da zargin cewa El-Rufai ya ƙirƙiri takardun shaidar zama ɗan jam’iyyar, tare da ƙoƙarin karkatar da harkokin cikin gida ta hanyar yaudara da dabara mara tsari.

  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Ra’ayoyin PDP, PRP Da SDP Kan Gudanar Da Zabe A Kano

Aiyenigba ya bayyana cewa El-Rufai bai taba yin rajista da SDP a matakin mazaɓarsa ba kamar yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tanada, amma ya sanar da jama’a a kafafen sada zumunta cewa ya shiga jam’iyyar, har ma ya ɗauki hoto da wasu jiga-jigan jam’iyyar da aka dakatar domin ƙarfafa wannan iƙirarin.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta ƙara da cewa duk da an nuna masa karamci sakamakon Muƙaminsa na baya a matsayin minista da gwamna, bincike ya tabbatar cewa bai cika sharuɗɗan zama mamba ba. A maimakon haka, yana ƙoƙarin mamaye jam’iyyar ne tare da wani shiri da ke haɗe shi da wata jam’iyya daban.

Har ila yau, SDP ta zargi El-Rufai da nuna gaba da jam’iyyar lokacin da yake kan mulki a ƙarƙashin APC da kuma yunƙurin amfani da SDP wajen cika burinsa na siyasa, duk da kasancewarsa da wata jam’iyyar daban (ADC).

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Jam’iyyar ta buƙaci hukumar INEC da sauran hukumomi da su lura cewa El-Rufai ba ɗan jam’iyyar ba ne, kuma bai da hurumin wakiltar ta a kowanne mataki. SDP ta kuma jaddada ƙudurinta na kare dimokuraɗiyya ta cikin gida da kuma adawa mai tushe da gaskiya.

SDP
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya
  • Abubakar Sulaiman
    INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
  • Abubakar Sulaiman
    Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

MASU ALAKA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
Rahotonni

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Next Post
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.