ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 55 Da Kulla Diflomasiyya: Akwai Kyakkawar Huldar Abota Tsakanin Sin Da Najeriya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Diflomasiyya

A yau ne ake cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen Sin da Najeriya. A wani bikin murnar ranar ta musamman da ya gudana a birnin Abuja a kwanakin baya, Joseph Tegbe, darekta-janar na kwamitin huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare ta Najeriya da Sin (NCSP), ya ce, hadin gwiwar da kasashen 2 suke yi ya zarce matsayin harkar diflomasiyya, tare da samar da dimbin sakamako masu amfanar da jama’a a zaman rayuwarsu na yau da kullum.

Cikin jawabinsa, Mista Tegbe ya ambaci wani sabon aikin kiwon kaji da aka kaddamar da shi a Najeriya a kwanan baya, wanda bangaren Sin ya samar da tallafi a ciki. Ana sa ran zuba dalar Amurka biliyan 1 wajen gudanar da aikin, inda za a yi kiwon kaji da yawansu ya kai fiye da miliyan 7, ta yadda za a rika samun kwai kimanin miliyan 6 a kowace rana, don samar da karin abinci ga mutanen Najeriya. Ban da haka, Mista Tegbe ya ambaci niyyar bangarorin Sin da Najeriya ta hadin gwiwa don sake gina masana’antar samar da karafa ta Ajaokuta, wadda a cewarsa za ta tabbatar da farfadowar masana’antar, da daidaita tsarin raya tattalin arzikin Najeriya, gami da mai da kasar ta zama cibiyar sarrafa kayayyaki ta nahiyar Afirka.

Haka zalika, a nasa bangare, wani mai nazarin al’amura masu alaka da kasashe masu tasowa na Najeriya mai suna Lawal Sale, ya rubuta wani bayani da ya shafi huldar dake tsakanin Najeriya da Sin, wanda aka wallafa a shafin kafar yada labaru ta “Economic Confidential”, inda ya bayyana huldar a matsayin mai samar da takamaiman sakamako. A cewarsa, bisa tsare-tsaren hadin gwiwa na “Ziri Daya Da Hanya Daya” da Dandalin Hadin Gwiwar Kasar Sin Da Kasashen Afirka, kasar Najeriya ta ci gajiyar dimbin ayyukan gina kayayyakin more rayuwar jama’a. A cikinsu har da layin dogo na Abuja-Kaduna, da na Lagos-Ibadan, da layin jirgin kasa na birnin Lagos, da na birnin Abuja, da tashar jiragen ruwa ta Lekki, da tagwan hanya ta Abuja-Keffi-Makurdi, da manyan gine-ginen zamani guda 6 da aka gina cikin wasu filayen tashi da saukar jiragen sama dake Najeriya, da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Shin me ya sa huldar dake tsakanin Sin da Najeriya ke iya samar da dimbin sakamako masu inganci kamar haka? Dalili shi ne, bisa matsayinsu na bai-daya na kasashe masu tasowa, Sin da Najeriya suna da burin iri daya, wato zamanantar da al’umma da kyautata zaman rayuwar jama’a. Saboda haka, ba sa yarda da manufar kasashen yammacin duniya ta mai da kansu “masu jagorantar duniya” da neman ta da rikici bisa bambancin tunanin siyasa. Saboda haka, a yayin da wata babbar kasa dake yammacin duniya ta dauki matakan da suka hada da kara harajin kwastam, da hana shigowar mutane cikin harabarta, da kakaba laifin “keta hakkin dan Adam”, da barazanar kai hari, kan Nijeriya, a nasu bangare, kasar Sin da ta Najeriya suna kallon juna a matsayin abokan hulda na daidai-wa-daida, inda suke samar da sakamako a-kai-a-kai, ta hanyar hadin gwiwa a fannonin gina kayayyakin more rayuwa, da ilimi, da kiwon lafiya, da aikin gona, da dai sauransu.

Zuwa yanzu, Najeriya ta zame wa kasar Sin babbar abokiyar hulda ta farko a fannin aikin gini, kuma kasa ta biyu a fannin karbar kayayyakin da kasar Sin ta kera da fitarwa zuwa ketare, da zama abokiyar ciniki ta uku, da wurin da ake zuba wa jari mai muhimmanci a nahiyar Afirka. Ya zuwa watan Nuwamban shekarar 2025, jimillar darajar cinikin da aka yi tsakanin Sin da Najeriya ta zarce dalar Amurka biliyan 22 da miliyan 300, wadda ta nuna yanayi na samun karuwa cikin matukar sauri.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A wannan lokacin da ake murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Najeriya, muna iya ganin yadda kasashen 2 ke ci gaba da zama ginshikai wajen samar da karuwa da hadin kai da kuma ci gaba a nahiyar Afirka, da tsarin hadin kan kasashe masu tasowa, da ma tsari na kasa da kasa.

Duk da cewa duniyarmu na cike da yanayin rashin tabbas, amma hadin gwiwar Sin da Najeriya yana ci gaba da samar da sakamako mai gamsarwa. Hakan ya shaida muhimmancin huldar abota ta daidai-wa-daida, da mutunta juna, da kokarin samar da sakamako mai inganci. (Bello Wang)

Diflomasiyya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Diflomasiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Na Yi Murabus Ne Saboda Dalilai Na Ƙashin Kaina – Shugaban Hukumar Aikin Hajji

Na Yi Murabus Ne Saboda Dalilai Na Ƙashin Kaina - Shugaban Hukumar Aikin Hajji

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.