ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 55 Da Kulla Diflomasiyya: Akwai Kyakkawar Huldar Abota Tsakanin Sin Da Najeriya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Diflomasiyya

A yau ne ake cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen Sin da Najeriya. A wani bikin murnar ranar ta musamman da ya gudana a birnin Abuja a kwanakin baya, Joseph Tegbe, darekta-janar na kwamitin huldar abota da ta shafi manyan tsare-tsare ta Najeriya da Sin (NCSP), ya ce, hadin gwiwar da kasashen 2 suke yi ya zarce matsayin harkar diflomasiyya, tare da samar da dimbin sakamako masu amfanar da jama’a a zaman rayuwarsu na yau da kullum.

Cikin jawabinsa, Mista Tegbe ya ambaci wani sabon aikin kiwon kaji da aka kaddamar da shi a Najeriya a kwanan baya, wanda bangaren Sin ya samar da tallafi a ciki. Ana sa ran zuba dalar Amurka biliyan 1 wajen gudanar da aikin, inda za a yi kiwon kaji da yawansu ya kai fiye da miliyan 7, ta yadda za a rika samun kwai kimanin miliyan 6 a kowace rana, don samar da karin abinci ga mutanen Najeriya. Ban da haka, Mista Tegbe ya ambaci niyyar bangarorin Sin da Najeriya ta hadin gwiwa don sake gina masana’antar samar da karafa ta Ajaokuta, wadda a cewarsa za ta tabbatar da farfadowar masana’antar, da daidaita tsarin raya tattalin arzikin Najeriya, gami da mai da kasar ta zama cibiyar sarrafa kayayyaki ta nahiyar Afirka.

Haka zalika, a nasa bangare, wani mai nazarin al’amura masu alaka da kasashe masu tasowa na Najeriya mai suna Lawal Sale, ya rubuta wani bayani da ya shafi huldar dake tsakanin Najeriya da Sin, wanda aka wallafa a shafin kafar yada labaru ta “Economic Confidential”, inda ya bayyana huldar a matsayin mai samar da takamaiman sakamako. A cewarsa, bisa tsare-tsaren hadin gwiwa na “Ziri Daya Da Hanya Daya” da Dandalin Hadin Gwiwar Kasar Sin Da Kasashen Afirka, kasar Najeriya ta ci gajiyar dimbin ayyukan gina kayayyakin more rayuwar jama’a. A cikinsu har da layin dogo na Abuja-Kaduna, da na Lagos-Ibadan, da layin jirgin kasa na birnin Lagos, da na birnin Abuja, da tashar jiragen ruwa ta Lekki, da tagwan hanya ta Abuja-Keffi-Makurdi, da manyan gine-ginen zamani guda 6 da aka gina cikin wasu filayen tashi da saukar jiragen sama dake Najeriya, da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Shin me ya sa huldar dake tsakanin Sin da Najeriya ke iya samar da dimbin sakamako masu inganci kamar haka? Dalili shi ne, bisa matsayinsu na bai-daya na kasashe masu tasowa, Sin da Najeriya suna da burin iri daya, wato zamanantar da al’umma da kyautata zaman rayuwar jama’a. Saboda haka, ba sa yarda da manufar kasashen yammacin duniya ta mai da kansu “masu jagorantar duniya” da neman ta da rikici bisa bambancin tunanin siyasa. Saboda haka, a yayin da wata babbar kasa dake yammacin duniya ta dauki matakan da suka hada da kara harajin kwastam, da hana shigowar mutane cikin harabarta, da kakaba laifin “keta hakkin dan Adam”, da barazanar kai hari, kan Nijeriya, a nasu bangare, kasar Sin da ta Najeriya suna kallon juna a matsayin abokan hulda na daidai-wa-daida, inda suke samar da sakamako a-kai-a-kai, ta hanyar hadin gwiwa a fannonin gina kayayyakin more rayuwa, da ilimi, da kiwon lafiya, da aikin gona, da dai sauransu.

Zuwa yanzu, Najeriya ta zame wa kasar Sin babbar abokiyar hulda ta farko a fannin aikin gini, kuma kasa ta biyu a fannin karbar kayayyakin da kasar Sin ta kera da fitarwa zuwa ketare, da zama abokiyar ciniki ta uku, da wurin da ake zuba wa jari mai muhimmanci a nahiyar Afirka. Ya zuwa watan Nuwamban shekarar 2025, jimillar darajar cinikin da aka yi tsakanin Sin da Najeriya ta zarce dalar Amurka biliyan 22 da miliyan 300, wadda ta nuna yanayi na samun karuwa cikin matukar sauri.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A wannan lokacin da ake murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Najeriya, muna iya ganin yadda kasashen 2 ke ci gaba da zama ginshikai wajen samar da karuwa da hadin kai da kuma ci gaba a nahiyar Afirka, da tsarin hadin kan kasashe masu tasowa, da ma tsari na kasa da kasa.

Duk da cewa duniyarmu na cike da yanayin rashin tabbas, amma hadin gwiwar Sin da Najeriya yana ci gaba da samar da sakamako mai gamsarwa. Hakan ya shaida muhimmancin huldar abota ta daidai-wa-daida, da mutunta juna, da kokarin samar da sakamako mai inganci. (Bello Wang)

Diflomasiyya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Diflomasiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Na Yi Murabus Ne Saboda Dalilai Na Ƙashin Kaina – Shugaban Hukumar Aikin Hajji

Na Yi Murabus Ne Saboda Dalilai Na Ƙashin Kaina - Shugaban Hukumar Aikin Hajji

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.