ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Kwalliya Za Ta Biya Kudin Sabulu Game Da Ziyarar Yellen A Wannan Karon?

by CGTN Hausa
2 years ago
Yellen

A yau Talata ne sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen ke kammala ziyararta a kasar Sin. Kuma da yammacin jiya Litinin, jami’ai masu ruwa da tsaki daga ma’aikatar kudi ta Sin sun yi karin haske game da ziyarar, inda suka tabo wasu batutuwa da Sin da Amurka suka amince da su. 

Daga cikin batutuwan da suka ja hankalina akwai aniyar kasashen ta samar da kyakkaywan yanayin kasuwanci da zuba jari. Zan iya cewa, an shafe lokaci mai tsawo tun lokacin mulkin tsohon shugaban Amurka Donald Trump, ake ta jayayya game da batutuwan da suka shafi yanayin cinikayya tsakanin manyan kasashen biyu, lamarin da bai haifar da komai ba sai koma baya har zuwa yanzu. Bangaren Amurka ya ci gaba da kakaba takunkumai da aiwatar da manufofi masu dakile ci gaban cinikayya tsakanin bangarorin biyu. Amma idan har a wannan karon Amurka za ta gyara kuskurenta, tare da samar da muhalli mai kyau na kasuwanci, to ba kasar Sin kadai ba, Amurkar da kamfanoninta za su amfana. Kyautata muhallin kasuwanci tsakaninsu zai bunkasa tattalin arzikinsu da samar da karin guraben ayyukan yi da tarin damarmakin hadin gwiwa da na ci gaba, har ma da more sabbin ci gaban kasar Sin, la’akari da yadda Sin din ta dade tana kira da kyautata huldar kasashen biyu domin moriyar juna. Haka kuma har kullum tana bude kofa tare da maraba da kamfanonin kasashen waje domin a samu ci gaba tare a duniya.

  • Xi Ya Amsa Wasikar Da Tawagar Jami’an ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Suka Aike Masa
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Asusun Merieux Na Kasar Faransa

Haka kuma sun amince da tabbatar da daidaito a tsakaninsu yayin da suke hadin gwiwa. Hadin gwiwar moriyar juna ba zai yuwu ba muddun wata kasa tana ganin ta fi wata. Haka kuma, ba za a taba samun kyautatuwar hulda ba muddun wata na son samun riba daga faduwar wata. Duk wata ‘yantacciyar kasa na bukatar a girmama dokoki da muradunta ko da kuwa karama ce. Idan ana son kyautata hulda tsakanin kasashen biyu, to ya zama wajibi kowacce ta girmama dayan. Kuma tabbatar da daidaito ya shafi kyale kowacce ta zabarwa kanta abun da ya fi dacewa da ita ba tare da suka ko shafa mata bakin fenti ba. Har ila yau, ya na nufin babu tsoma baki ko katsalandan game da yadda kowacce kasa ta zabi tafiyar da harkokinta na cikin gida. Don haka, kamata ya yi Amurka ta nuna da gaske take, ta girmama zabin kasar Sin da yadda take gudanar da harkokinta na gida, domin ita ta fi sanin abun da ya dace da ita da al’ummarta.

ADVERTISEMENT

Wani batu kuma shi ne tsaro. Tsaron kasa babban batu ne ga kowacce kasa, sai dai bai kamata a rika fakewa da ita wajen dakilewa ko hana ci gaban wata kasa ba. Ya kamata duk wani zargin barazana ga tsaron kasa ya kasance bisa tushe na gaskiya da kuma adalci. Bai kamata wannan batu ya rika zama makamin tada fitina ko takala ba.

A jawabin da Janet Yellen ta gabatar ga manema labarai, ta jaddada cewa kasarta ba ta da niyyar raba gari da Sin, tana mai kiran Sin din a matsayin babbar kasuwa ga hajoji da hidimomin Amurka, tana mai cewa tattalin arzikin kasashen biyu na hade da juna. Zancenta haka yake, sai dai abun jira a gani shi ne ko a wannan karon, za a ga irin wannan furuci a aikace. Lokaci ya yi da ya kamata Amurka ta rika aiwatar da abun da take fada maimakon fadin wani abu daban, sannan ta aikata wani abu na daban.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Yellen
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Ana Fatan Amurka Za Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Bayan Ziyarar Janet L. Yellen A Sin

Ana Fatan Amurka Za Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Bayan Ziyarar Janet L. Yellen A Sin

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.