Ɓangaren jam’iyyar PDP a ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki ya bayyana cewa zai amince da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa gabanin zaben 2027 a wani taron ƙasa na musamman da za a gudanar ranar Asabar a Abuja.
A cewar gayyatar taron da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar, Ini Ememobong, da sakataren shirye-shirye na ƙasa, Theophilus Dakas Shan, suka sanya wa hannu, taron zai gudana ranar 30 ga Mayu, 2026 domin tabbatar da tsayar da Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na ɓangaren PDP.
Ana sa ran shugabannin jam’iyya, wakilai da mambobi daga sassan ƙasar nan za su halarci taron wanda ɓangaren jam’iyyar ke gani a matsayin wani babban mataki a shirye-shiryensu na zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.
Sai dai zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Goodluck Jonathan bai fito fili ya amince da takarar ko bayyana aniyarsa ta tsayawa takara a zaɓen 2027 ba. A wani taro da matasa a Abuja kwanan nan, ya ce takarar shugaban ƙasa “ba wasan kwamfuta ba ne,” yana mai cewa zai tuntuɓi mutane kafin ɗaukar matsaya.
A ɓangaren guda kuma, ɓangaren PDP mai biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, tuni ya amince da Sandy Onor a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na ɓangaren nasu.















Discussion about this post