Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya zanta da takwaransa na Kyrgyzstan Sadyr Japarov a yau Litinin. Yayin tattaunawar tasu, shugaba Xi ya ce cikin ‘yan shekarun baya bayan nan, manyan ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasarsa da Kyrgyzstan, ciki har da layin dogo na Sin zuwa Kyrgyzstan zuwa Uzbekistan na ci gaba da gudana yadda ya kamata, suna kuma mara baya ga ci gaban kasashen biyu, tare da haifar da alfanu ga al’ummunsu, kana suna ingiza zaman lafiya, daidaito da walwala a yankinsu.
Kazalika, shugaba Xi ya ce kasarsa na yin duk mai yiwuwa wajen lalubo ‘yan kasar da ma na ketare da suka bace, sakamakon ibtila’in zabtarewar kasa da ya auku a jihar Xizang mai cin gashin kai ta Sin. Har ila yau, Sin na aiwatar da dukkanin matakan da suka wajaba na ganowa da tsugunar da wadanda ibtila’in ya shafa, tare da samar da tallafin jinya ga wadanda suka jikkata, da ma kandagarkin mummunan tasirin da ibtila’in ka iya haifarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














