ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙin Iran: Bankin Duniya Ya Yi Gargadin Tashin Farashin Takin Zamani

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Iran

Farashin man fetur da takin zamani a duniya suna kan hanyar tashin goron zabi a cikin shekaru hudu, yayin da yakin Iran ke ci gaba da girgiza kasuwannin kayan masarufi, in ji Bankin Duniya a cikin sabuwar rahoton hasashen kasuwannin kayan masarufi.

Babban Bankin Duniya, a ranar Talata ya gargadin cewa farashin makamashi na iya tashi da kashi 24 cikin dari a wannan shekara, wanda zai zama mafi girma tun lokacin da rikicin ya barke da mamayar Rasha a Ukraine.

Ana hasashen cewa farashin kaya gaba daya zai karu da kashi 16 cikin dari a shekarar 2026, wanda mafi yawanci abin ya samo asali ne daga tsananin karuwa a farashin makamashi da taki, da matakan mafi girma da aka taba samu a wasu muhimman tashoshi.

ADVERTISEMENT

A cewar rahoton, girgizan da ke fitowa daga rikicin Gabas ta Tsakiya ya fara yaduwa a cikin hanyoyin samar da kayayyaki na duniya, tare da manyan tasiri ga ci gaban tattalin arziki, samar da ayyuka da ci gaba, musamman a kasuwanni masu tasowa.

A tsakiyar wannan tashin hankali akwai mashigin Hormuz, wata muhimmin hanyar sufuri ta ruwa da ke daukar kusan kashi 35 cikin dari na kasuwancin mai na duniya ta teku. Hare-hare kan abubuwan more rayuwa na makamashi da cunkoson sufuri a wannan hanya sun haddasa abin da Babban Bankin Duniya ya bayyana a matsayin mafi girman girgizar samar da mai a tarihi, inda aka rage samar da mai a duniya da kusan ganga miliyan 10 a rana a lokaci mafi tsananin tashin hankali.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ko da yake farashin ya ragu kadan daga mafi girman matakan da aka samu kwanan nan, farashin danyan mai ya kasance sama da kashi 50 cikin dari fiye da matakan da aka samu a farkon shekara a tsakiyar Afrilu.

Bankin ya yi hasashen cewa dayan mai zai kai matsakaicin na dala 86 a kowace ganga a shekarar 2026, daga dala 69 a shekarar 2025, idan aka dauka cewa manyan tangarda sun ragu a cikin watanni masu zuwa kuma hanyoyin ruwa suna dawowa daidaito a hankali.

Babban masanin tattalin arziki na Bankin Duniya, Indermit Gill, ya yi gargadin cewa rikicin na bayyana a matakai daban-daban, tare da tasiri mai girma.

“Yakin na shafar tattalin arzikin duniya a cikin hanyoyi daban-daban, farko ta hanyar hauhawar farashin makamashi, sannan hauhawar farashin abinci, da kuma hauhawar farashin kayayyakin abinci, wanda zai kara kudin ruwa na bashi kuma ya sanya bashi ya fi tsada.

“Mutanen da suka fi talauci wadanda ke kashe mafi yawan kudaden shigarsu kan abinci da man fetur, za su fi shiga matsala, kamar yadda kasashe masu tasowa ke fama da matsalolin bashi. Duk wannan tunatarwa ce game da koma-bayan da yakin ya haddasa “, in ji shi.

Ana sa ran farashin taki zai tashi da kashi 31 cikin dari a shekarar 2026, wanda hakan zai faruwa ne saboda tashin farashin urea da kashi 60 cikin dari. Ana hasashen wannan zai sa samun taki a ya kai mafi rauni tun daga shekarar 2022, yana matsa lamba ga ribar manoma kuma yana barazanar ga samar da amfanin gona.

Rahoton ya yi gargadin cewa idan rikicin ya yi tsawo na iya kara tsananta rashin abinci a duniya, inda Shirin samar da abinci na duniya ke kiyasta cewa mutane miliyan 45 za su shiga cikin yunwa mai tsanani idan matsin lamba na samar da abinci ya ci gaba.

Babban Bankin Duniya ya kara cewa tashin farashin kayan masarufi zai karfafa matsin lamba na hauhawar farashin kayayyaki kuma ya raunana ci gaban tattalin arzikin duniya.

Hawan farashin kayayyaki a kasuwannin da ke tasowa yanzu an kiyasta zai kai kashi 5.1 a cikin dari a shekarar 2026, daga kashi 4.7 a cikin dari. Ana sa ran ci gaban tattalin arziki a wadannan kasuwanni zai ragu zuwa kashi 3.6 a cikin dari, wani sauyi ne zuwa kasa daga hasashen da aka yi a baya.

Mataimakin babban masanin tattalin arziki na Bankin Duniya, Ayhan Kose, ya yi kira ga masu tsara manufofi da su yi taka tsantsan wajen mayar da martani ga rikicin da ke faruwa.

“Tashin hankali da ya biyo baya cikin shekara goma ya rage tsarin kudi da ake da shi don mayar da martani kan rikicin samar da makamashi na tarihi da ake ciki yanzu.

“Dole ne gwamnatoci su ki yin amfani da manyan matakan tallafin kudi marasa ma’ana wadanda za su iya lalata kasuwanni kuma su rage ajiyar kudi na gwamnati. Maimakon haka, su mayar da hankali kan tallafi cikin sauri da na dan lokaci wanda aka tsara musamman ga gidajen da suka fi rauni,” in ji shi.

Iran
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
2027:Atiku Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Ya Janye Takararsa Ya Mara Wa Obi Da Kwankwaso Baya

2027:Atiku Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Ya Janye Takararsa Ya Mara Wa Obi Da Kwankwaso Baya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.