A yau Litinin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da cewa, bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaban kasar Amurka Donald Trump zai ziyarci Sin daga ranar 13 zuwa 15 ga watan nan na Mayu.
Ziyarar shugaban Amurka ta baya-bayan nan zuwa Sin, ita ce ta farko tun bayan ta shekarar 2017. A wancan karo, shugaban Amurkan Trump ya ziyarci kasar Sin ne daga ranar 8 zuwa 10 ga watan Nuwamban 2017.Tattaunawar manyan shugabannin kasashen biyu, na taka muhimmiyar rawa da ba za a iya maye gurbinta ba a dangantakar Sin da Amurka.
A cikin fiye da shekara guda tun bayan tazarcen Trump a matsayin shugaban Amurka, manyan shugabannin Sin da Amurka sun yi muhimman mu’amala har sau 7.
A yayin tattaunawa ta wayar tarho ta baya-bayan nan tsakaninsa da shugaba Trump, shugaba Xi ya ce ya kamata bangarorin biyu su yi biyayya ga yarjejeniyar da suka cimma, da karfafa tattaunawa da tunbubar juna, da kuma shawo kan sabanin ra’ayi tsakaninsu yadda ya kamata, kana su fadada hadin gwiwa mai amfani.
Ya kuma kara da cewa, dole ne su yi aiki daya bayan daya, don wanzar da amincewa da juna sannu a hankali, ta yadda za a samar da hanya da ta dace ta dorewar zaman tare cikin lumana, wanda hakan zai taka rawar gani wajen sanya shekarar 2026 ta zama shekarar mutunta juna, zaman lafiya tare da hadin gwiwa mai amfani ga juna tsakanin manyan kasashen biyu wato Sin da Amurka. (Amina Xu)















Discussion about this post